< Ezekiel 32 >
1 On the first day of the twelfth month of the twelfth year, a message from the Lord came to me, saying,
A shekara ta goma sha biyu, a wata na goma sha biyu a rana ta fari, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, sing a funeral song for Pharaoh king of Egypt and tell him: You think you're like a lion among the nations but in reality you're like a sea monster. You roll around in your rivers, stirring up the waters with your feet, making the water muddy.
“Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir’auna sarkin Masar ka faɗa masa. “‘Kai kamar zaki ne a cikin al’ummai; kai kamar dodon ruwa a cikin tekuna kana ɓullowa cikin rafuffukanka, kana gurɓata ruwa da ƙafafunka kana kuma dama rafuffuka.
3 This is what the Lord God says: In the presence of many nations I'm going to spread my net over you, and they will pull you up in my net.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Da taron jama’a masu yawa zan jefa abin kamun kifi a kanka, za su kuwa jawo ka da abin kamun kifi.
4 I will drop you on the land; I will throw you down on the bare earth. I will make all the birds of prey come and land you; I will have all the wild animals eat you until they're satisfied.
Zan jefar da kai a ƙasa zan jefa ka a fili. Zan sa dukan tsuntsayen sararin sama su zauna a kanka dukan namun jeji na duniya kuma za su ƙosar da kansu a kanka.
5 I will dump your flesh on the mountains and fill the valleys with your remains.
Zan baza namanka a kan duwatsu in kuma cika kwaruruka da gawarka.
6 I will fill the land with your flowing blood, pouring it out on the mountains, filling the valleys.
Zan jiƙa ƙasar da jininka mai gudu har zuwa duwatsu, magudanan ruwa za su cika da namanka.
7 When I put out the light of your life, I will cover the heavens and darken their stars. I will use a cloud to cover the sun, and the moon will stop shining.
Sa’ad da na shafe ka, zan rufe sammai in duhunta taurarinsu; zan rufe rana da girgije, wata kuwa ba zai ba da haskensa ba.
8 I will darken all the bright lights in the heavens above you, and I will make your land go dark, declares the Lord God.
Dukan haskokin sammai za su zama duhu a kanka; zan kawo duhu a kan ƙasarka, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 When I destroy you I will make many people frightened, even in countries you don't know anything about.
Zan dami zukatan mutane masu yawa sa’ad da na kawo maka hallaka a cikin al’ummai, a cikin ƙasashen da ba ka taɓa sani ba.
10 Many will be shocked at what I do to you, and their kings will be horrified at what has happened to you, trembling when I wave my sword in front of them. On the day that you fall all of them will shake in fear for their lives.
Zan sa mutane da yawa su giggice saboda abin da ya same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa’ad da na kaɗa takobina a gabansu. A ranar fāɗuwarka kowannensu zai yi rawar jiki a kowane lokaci saboda ransa.
11 For this is what the Lord God says: The sword of the king of Babylon will attack you!
“‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Takobin sarkin Babilon zai auko maka.
12 I will allow your army to be defeated, your soldiers killed by the swords of the powerful enemy army from the cruelest of all nations. They will ruin of the glories of Egypt and destroy all your people.
Zan sa jama’arka su mutu ta wurin takuban ƙarfafan mutane, masu bantsoro na dukan al’ummai. Za su lalatar da girman kan Masar, su kuma tumɓuke dukan jama’arta.
13 I will slaughter all your livestock living beside the wide rivers. Nobody will be there to stir rivers up with their feet; no livestock hooves will make them muddy.
Zan hallaka dukan dabbobinta da suke kusa da ruwaye masu yawa ƙafar mutum ba zai ƙara damunsa ko kofaton dabba ya gurɓata shi.
14 I will allow their waters to settle and I will make her rivers flow smoothly like oil, declares the Lord God.
Sa’an nan zan sa ruwanta su kwanta in sa rafuffukanta su gudu kamar mai, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 When I turn Egypt into a wasteland, completely emptying it out, when I kill everyone who lives there, then they will acknowledge that I am the Lord.
Sa’ad da na mai da Masar kufai na kuma raba ƙasar da abin da take cike da shi, sa’ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta, a sa’an nan ne za su san cewa ni ne Ubangiji.’
16 This is the funeral song that foreign women will sing. They will sing it in mourning over Egypt and all its many people, declares the Lord God.”
“Wannan ne makokin da za a yi mata.’Yan matan al’ummai za su rera shi; gama Masar da dukan jama’arta za su rera shi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
17 On the fifteenth day of the twelfth month of the twelfth year, a message from the Lord came to me, saying,
A shekara ta goma sha biyu, a rana ta goma sha biyar ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 “Son of man, weep for all the many Egyptians. Send them along with the people of powerful nations down into the depths of the earth with those who go down into the grave.
“Ɗan mutum, yi kuka saboda jama’ar Masar ka kuma tura ta da’yan matan manyan al’ummai zuwa ƙarƙashin ƙasa, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
19 Do you think you're more beautiful than anyone else? Go down and take your place in the grave with the heathen!
Ka ce, ‘Kin fi sauran tagomashi ne? Ki gangara, ki kwanta cikin marasa kaciya.’
20 They will lie among those killed by the sword. A sword is ready to kill all the many people of Egypt.
Za su fāɗi cikin waɗanda aka kashe da takobi. Takobin da an zāre; bari a ja ta a tafi tare da dukan jama’arta.
21 Powerful chiefs will speak from Sheol about Egypt and its allies: ‘They have come down here and lie with the heathen, with those killed by the sword.’ (Sheol )
Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol )
22 Assyria is there with all its people—it's surrounded by graves. All of them died violent deaths, killed by the sword.
“Assuriya tana can tare da dukan sojojinta; an kewaye ta da kaburburan dukan waɗanda aka kashe, dukan waɗanda suka mutu ta wurin takobi.
23 Its graves are set in the deepest parts of the place of the dead, and the graves of all its people surround Assyria's grave. All of them died violent deaths, killed by the sword, these people who once terrorized others when they were alive.
Kaburburansu suna cikin zurfafan rami kuma sojojinta suna kwance kewaye da kabarinta. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun mutu, an kashe su da takobi.
24 Elam is there with all its people around its grave. All of them died violent deaths, killed by the sword. They went down into the grave, these heathen people who once terrorized others when they were alive. They are disgraced, along with all others who go down into the grave.
“Elam tana can, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu sun mutu, an kashe su da takobi. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun gangara wurin marasa kaciya a duniyar da take ƙarƙashi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
25 A resting place is made ready among those who have been killed for Elam and all its many people—their graves surround Elam's grave. They are all heathen and were killed by the sword, though they once terrorized others when they were alive. They are disgraced, along with all others who go down into the grave. They are laid to rest among those who have been killed.
An yi mata gado a cikin matattu, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi. Domin tsoronsu ya bazu cikin ƙasar masu rai, suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami; an kwantar da su tare da waɗanda aka kashe.
26 Meshech and Tubal are there with all their many people, surrounded by all their graves. They are all heathen and were killed by the sword, though they once terrorized others when they were alive.
“Meshek da Tubal suna can, tare da dukan jama’arsu kewaye da kaburburansu. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi domin sun haddasa tsoronsu a ƙasar masu rai.
27 But they're not laid to rest with the fallen warriors of long ago who went down into Sheol with their weapons of war. Their swords were placed underneath their heads and their shields over their bones, although these powerful warriors once terrorized others when they were alive. (Sheol )
Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol )
28 However, you will also be cut down and laid to rest with the heathen, with those killed by the sword.
“Kai kuma, ya Fir’auna, za a kakkarye ka za ka kuma kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.
29 Edom is there with all its kings and princes. Once they were powerful, but now they too are laid to rest with those killed by the sword. They lie with the heathen, with those who go down into the grave.
“Edom tana can, sarakunanta da dukan yerimanta; duk da ikonsu, sun kwanta tare da waɗanda aka kashe da takobi. Suna kwance tare da marasa kaciya, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
30 All the leaders from the north, and all the people of Sidon are there too. They also are disgraced, going down with those who were killed, in spite of their formidable power. They are heathen, lying there with those killed by the sword, and have the disgrace of those who go down into the grave.
“Dukan yerima arewa da dukan Sidoniyawa suna can; sun gangara tare da waɗanda aka kashe cikin kunya duk da tsoron da suka haddasa ta wurin ikonsu. Sun kwanta tare da marasa kaciya tare da waɗanda aka kashe da takobi suna kuma shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
31 Pharaoh will see them and be pleased that he and all his many people are not the only ones killed by the sword, declares the Lord God.
“Fir’auna, shi da dukan sojojinsa, za su gan su zai kuma ta’azantu domin dukan jama’arsa da aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
32 For I will terrorize those who are alive so that Pharaoh and all his many people will be laid to rest with the heathen, with those killed by the sword, declares the Lord God.”
Ko da yake na sa ta haddasa tsoro a ƙasar masu rai, Fir’auna da dukan jama’arsa za su kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”