< Exodus 31 >

1 The Lord told Moses,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “I have chosen by name Bezalel, son of Uri, son of Hur, from the tribe of Judah.
“Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
3 I have filled him with the Spirit of God giving him ability, creativity, and expertise in all kinds of craftsmanship.
na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
4 He can produce designs in gold, silver, and bronze,
don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
5 he can cut gemstones to place in settings, and he can carve wood. He is a master of every craft.
don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
6 I have also chosen Oholiab, son of Ahisamach, from the tribe of Dan, to help him. I have also given all the craftsmen the skills needed to make everything that I have ordered you to make:
Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
7 the Tent of Meeting, the Ark of the Testimony and its atonement cover, and all the other furniture in the Tent:
Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
8 the table with its equipment, the pure gold lampstand with all its equipment, the altar of incense,
tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
9 the altar of burnt offering with all its utensils, and the basin plus its stand;
bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
10 as well as the woven clothes for both Aaron the priest and for his sons to serve as priests,
da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
11 as well as anointing oil and fragrant incense for the Holy Place. They are to make them following all the instructions I have given you.”
da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
12 The Lord told Moses,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
13 “Tell the Israelites, ‘It's absolutely essential that you keep my Sabbaths. The Sabbath will be a sign between me and you for generations to come, so that you'll know that I am the Lord who makes you holy.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
14 You shall keep the Sabbath because it is holy to you. Anyone who dishonors it must be killed. Anyone who works on that day must be cut off from their people.
“‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
15 Six days you can work, but the seventh day is to be a Sabbath of rest, holy to the Lord. Anyone who does any work on the Sabbath day must be killed.
Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
16 The Israelites must keep the Sabbath, observing the Sabbath as an everlasting agreement for generations to come.
Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
17 It's a sign between me and the Israelites forever, for the Lord made the heavens and the earth in six days, but on the seventh day he stopped and he rested.’”
Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
18 When the Lord finished speaking with Moses on Mount Sinai, he gave him the two tablets of the Testimony, stone tablets written on by the finger of God.
Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.

< Exodus 31 >