< Deuteronomy 2 >

1 Then we turned around and headed back into the desert on the road that leads to the Red Sea, as the Lord had told me, and we wandered around Mount Seir for a long time.
Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
2 This is when the Lord told me,
Sai Ubangiji ya ce mini,
3 “You have been wandering around this mountain long enough. Go back north,
“Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
4 and give these orders to the people: ‘You are going to pass through the territory of your relatives, the descendants of Esau, who live in Seir. They will be frightened of you, so you need to be very careful.
Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
5 Don't fight them, for I'm not going to give you any of their land, not even the size of a footprint, because I have given Mount Seir to Esau and it belongs to him.
kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
6 Pay them with money for the food you eat and the water you drink.’
Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
7 Remember that the Lord your God has blessed you in everything you've done. He has looked after you during your journey through this large desert. The Lord your God has been with you for these forty years, and you haven't lacked anything.”
Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
8 So we passed by our relatives, the descendants of Esau, who live in Seir. We didn't take the Arabah road from Elath and Ezion-geber. Instead we used the road that goes through the desert of Moab.
Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
9 Then the Lord told me, “Don't cause the Moabites any trouble or fight them, for I'm not going to give you any of their land, because I have given Ar to the descendants of Lot and it belongs to them.”
Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
10 (A strong and numerous people called the Emim once lived there. They were as tall as the Anakim,
(Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
11 and just like the Anakim, they were also considered as Rephaim, but the Moabites called them Emim.
Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
12 Previously the Horites lived in Seir, but the descendants of Esau took over their land. They killed the Horites and settled there, just like Israel did when they occupied the land that the Lord had given them.)
Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
13 Then the Lord told us, “Go and cross over Zered Brook.” So we crossed over Zered Brook.
Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
14 The time it took for us to travel from Kadesh-barnea to when we crossed over the Brook of Zered was thirty-eight years. By this time the entire generation of warriors had died and were no longer part of the camp, as the Lord had sworn to them would happen.
Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
15 In fact the Lord worked against them to remove them from the camp, until they were all dead.
Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
16 Once the people's warriors had died,
To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
17 the Lord told me,
sai Ubangiji ya ce mini,
18 “Today you will cross out of Moab at the border near Ar.
“Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
19 However, when you get enter Ammonite territory, don't cause them any trouble or fight them for I'm not going to give you any Ammonite land, because I have given it to the descendants of Lot and it belongs to them.”
Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
20 (This land was previously considered as the country of the Rephaim who used to live there. However, the Ammonites called them Zamzummites.
(Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
21 They were a strong and numerous people, as tall as the Anakim. But the Lord destroyed them when the Ammonites invaded and drove them out and settled there,
Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
22 just as he'd done for the descendants of Esau who lived in Seir when he destroyed the Horites. They drove them out and settled where they used to live, and are still there to this day.
Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
23 The Avvim, living in villages as far away as Gaza, were destroyed by the Philistines, who came from Crete, and settled where they used to live.)
Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
24 Then the Lord told us, “Get up, go and cross the Arnon Valley. Look, I have handed over to you Sihon the Amorite, king of Heshbon, as well as his land. Go and start taking it over, and fight him in battle.
“Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
25 From this day on, I'm going to make all nations on earth dread you—they will be terrified of you. Because of the news they hear about you they will tremble in terror when you appear.”
A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
26 Moses told the Israelites, “From the Kedemoth Desert I sent messengers with an offer of peace to Sihon, king of Heshbon, telling him,
Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
27 ‘Let us pass through your land. We'll stay on the main road and won't turn off either to the right or to the left.
“Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
28 Sell us food to eat and water to drink for money. Just let us pass through on foot,
Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
29 just like the descendants of Esau living in Seir and the Moabites living in Ar allowed us, until we cross over the Jordan into the country that the Lord our God is giving to us.”
kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
30 But Sihon king of Heshbon refused to let us pass through, for the Lord your God gave him a stubborn spirit and an obstinate attitude, so the Lord could hand him over to you, as he has now done.
Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
31 Then the Lord told me, “Look, I have started handing Sihon and his land over to you. Now you can begin to conquer and take over his land.”
Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
32 Sihon and his whole army came out to fight us at Jahaz.
Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
33 The Lord our God handed him over to us, and we killed him, his sons, and all his army.
sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
34 We also captured all his towns, and set apart for destruction the people of every town: men, women, and children. We didn't leave any survivors.
A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
35 All we took for ourselves was the livestock and plunder from the towns we'd captured.
Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
36 No town had walls too high for us to conquer—from Aroer on the edge of the Arnon Valley, the town in the valley, all the way to Gilead. The Lord our God handed them all over to us.
Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
37 But you didn't go anywhere near the country of the Ammonites—the area that borders the Jabbok River or the towns of the hill country, or any other place that the Lord our God had placed off limits.
Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.

< Deuteronomy 2 >