< Amos 8 >

1 This is what the Lord God showed me. I saw a basket of fruit.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji ya nuna mini kwandon nunannun’ya’yan itace.
2 He asked me, “What do you see, Amos?” I said, “A basket of fruit.” Then the Lord told me, “This is the end of my people Israel! I won't ignore their sins anymore.
Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
3 On that day the Temple songs will become sorrowful wailing. There will be dead bodies scattered everywhere. Silence!” declares the Lord.
“A ranan nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Waƙoƙin a haikali za su koma makoki. Za a ga gawawwaki a ko’ina! Shiru!”
4 Listen to this, you who trample down the needy, and wipe out the poor of the land.
Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata kuka kori matalautan ƙasar.
5 You who ask, “When will the holy day be over so we can get back to selling grain? When will the Sabbath be over so we can open our storehouses, and cheat people with short measures and unfair scales?”
Kuna cewa, “Yaushe Sabon Wata zai wuce don mu sayar da hatsi, Asabbaci ta wuce, don mu sayar da alkama?” Mu yi awo da ma’aunin zalunci mu ƙara kuɗin kaya mu kuma cutar da mai saya,
6 You buy the poor for silver, the needy for a pair of sandals, and you sell grain mixed with chaff.
mu sayi matalauta da azurfa masu bukata kuma da takalmi, mu sayar da alkamar haɗe da yayi.
7 The Lord God, of whom the descendants of Jacob are so proud, has sworn an oath: I will never forget the evil you have done.
Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
8 Shall not the land tremble because of this, and everyone who lives there mourn? The earth will rise up like the Nile river in flood, be tossed around, and then fall again.
“Shin, ƙasar ba za tă yi rawan jiki saboda wannan ba, kuma duk masu zama a cikinta ba za su yi makoki ba? Ƙasar duka za tă hau ta sauka kamar Nilu; za a dama ta sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar.
9 On that day, declares the Lord God, I will make the sun go down at noon, and darken the land during the daytime.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Zan sa rana ta fāɗi da tsakar rana in kuma duhunta duniya da rana tsaka.
10 I will turn your festivals into times of mourning, your happy songs into laments. I will make you wear sackcloth and shave your heads. I will make your mourning like that for an only son. At the end of it all it will be a bitter day.
Zan mai da bukukkuwanku na addini su zama makoki kuma dukan waƙoƙinku su zama kuka. Zan sa dukanku ku sa rigunan makoki za ku kuma aske kawunanku. Zan sa wannan lokaci yă zama kamar lokacin da ake makokin ɗan tilon da ake da shi kuma ƙarshenta kamar rana mai ɗaci.
11 The time is coming, declares the Lord, when I will send a famine on the land—not a famine of bread, or a lack of water, but a famine of hearing the words of the Lord.
“Ranakun suna zuwa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “sa’ad da zan aika da yunwa cikin ƙasar, ba yunwar abinci ko ta ƙishirwa ba, sai dai yunwa ta jin maganar Ubangiji.
12 People will wander from sea to sea, from north to east, running to and fro searching for the word of the Lord, but they will not find it.
Mutane za su yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku suna yawo daga arewa zuwa kudu, suna neman maganar Ubangiji, amma ba za su samu ba.
13 On that day, even the beautiful girls and healthy young men will collapse from thirst.
“A wannan rana “kyawawan’yan mata da kuma samari masu ji da ƙarfi za su suma don ƙishirwa.
14 Those who swear by the disgraceful idols of Samaria, who take oaths like, “By the life of your god, Dan,” or “A pilgrimage to the god of Beersheba”—they will fall, and never rise again.
Waɗanda suka yi rantsuwa da abin kunya na Samariya, ko kuma su ce, ‘Muddin allahnku yana a raye, ya Dan,’ ko kuwa, ‘Muddin allahn Beyersheba yana a raye,’ za su fāɗi, ba kuwa za su ƙara tashi ba.”

< Amos 8 >