< Acts 24 >

1 Five days later Ananias the high priest arrived with some of the Jewish leaders, and with a lawyer called Tertullus. They presented formal charges against Paul to the governor.
Bayan kwanaki biyar, sai Ananiyas babban firist, Wasu dattawa da wani masanin shari'a mai suna Tartilus, sun tafi can. Suka kai karar Bulus gaban gwamna.
2 When Paul was summoned, Tertullus began making his case against him. He said, “Your Excellency Governor Felix, we have enjoyed a long period of peace under you, and as a result of your wise judgment reforms have been enacted for the benefit of the nation.
Lokacin da Bulus ya tsaya gaban gwamna, Tartilus ya fara zarginsa yace wa gwamnan, “Saboda kai mun sami zaman lafiya; sa'annan hangen gabanka ya kawo gyara a kasarmu;
3 All of us throughout the country are so very grateful to you for this.
don haka duk abin da ka yi mun karba da godiya, ya mai girma Filikus.
4 But in order not to bore you, please be so kind as to give us your attention for a short while.
Domin kada in wahalsheka, ina roko a yi mani nasiha don in yi magana kadan.
5 We discovered that this man is a real pest, stirring up rebellions among Jews all over the world, a ringleader of the Nazarene sect.
An iske mutumin nan yana barna irir iri, yana kuma zuga jama'ar Yahudawa a dukan duniya su yi tayarwa.
6 He tried to defile the Temple, so we arrested him.
Har ma ya yi kokarin kazantar da haikali; saboda haka muka kama shi. [Mun so mu shari'anta masa bisa ga dokarmu.]
7
Amma Lisiyas jami'i ya zo ya kwace shi da karfi daga hannunmu.
8 By interrogating him yourself you will discover the truth of our accusations.”
Idan ka binciki Bulus game da wadannan al'amura, kai ma, zai tabbatar maka abin da muke zarginsa a kai.
9 The Jews joined in, saying that this was all true.
Dukan Yahudawa suna zargin Bulus cewa wadannan abubuwa gaskiya ne.
10 The Governor motioned for Paul to respond. “Recognizing you have been a judge over this nation for many years, I gladly make my defense,” Paul began.
lokacin da gwamnan ya alamta wa Bulus ya yi magana sai yace, “Yanzu na fahimci cewar da dadewa kana mulkin kasarnan, don haka da farin ciki zan yi maka bayani.
11 “You can easily verify that I arrived in Jerusalem to worship just twelve days ago.
Zaka iya tabbatarwa cewa bai kai kwana sha biyu ba tun da nake zuwa Urushalima don yin sujada.
12 Nobody found me arguing in the Temple with anyone, or inciting people to riot in any synagogue or anywhere in the city.
Da suka same ni a haikali, ban yi jayayya ko kawo rudami a tsakanin jama'a ba.
13 Nor can they prove to you any of their accusations against me.
Don haka ba su da tabbas akan abinda suke zargina a kansa yau.
14 But I will admit this to you: I serve the God of our fathers following the beliefs of the Way, which they call a heretical sect. I believe everything the law teaches and what is written in the books of the prophets.
Amma na sanar da kai, bisa ga abin da suke kira darika, haka ni ma nake bautawa Allah na kakanninmu. Na yi aminci wajen kiyaye dukan abin da ke a rubuce a Attaurat da litattafan annabawa.
15 I have the same hope in God that they do, believing that there will be a resurrection of the good and the wicked.
Ina sa bege ga Allah, kamar yadda za a yi tashin matattu, masu adalci da miyagu;
16 Consequently I try to make sure I always have a clear conscience before God and everyone.
a kan haka kuma, nake kokarin zama mara abin zargi a gaban Allah da mutane ina yin haka cikin dukan al'amura.
17 Having been away for a few years I returned to bring some money to help the poor and to give offerings to God.
Bayan wadansu shekaru na zo in kawo wasu sadakoki da baikon yardar rai.
18 That's what they found me doing in the Temple—completing the ceremony of purification. There was no crowd and no disturbance.
Cikin kudurin yin haka, sai wasu Yahudawa daga kasar Asiya suka iske ni a cikin ka'idodin tsarkakewa a haikali, ba da taro ko ta da hargitsi ba.
19 But some Jews from the province of Asia were there, who should be present here before you today to bring their charges, if they have anything against me.
Yakamata wadannan mutanen su zo gabarka a yau, har idan suna da wani zargi a kai na.
20 Otherwise let these men here explain themselves what crime they found me guilty of when I stood before the council,
In kuwa ba haka ba bari mutanennan su fada in sun taba iske ni da wani aibu a duk lokacin da na gurfana a gaban majalisar Yahudawa;
21 except for the time when I shouted out to them, ‘I am on trial before you today because of my belief in the resurrection of the dead.’”
sai dai ko a kan abu daya da na fada da babbar murya sa'adda na tsaya a gabansu, 'Wato batun tashin matattu wanda ake tuhumata ake neman yi mani hukunci yau.'”
22 Felix who was well-informed about the Way then adjourned the trial. “When Lysias the commander comes I will make my decision regarding your case,” he said.
Filikus yana da cikakken sanin tafarkin Hanyar, shi yasa ya daga shari'ar. Yace da su, “Duk sa'anda Lisiyas mai ba da umarni ya zo daga Urushalima, zan yanke hukunci.”
23 He ordered the centurion to keep Paul in custody but to allow him some measure of freedom and to let Paul's friends care for him without interference.
Sa'annan ya umarci jarumin ya lura da Bulus, amma ya yi sassauci, kada ya hana abokansa su ziyarce shi ko su taimake shi.
24 Some days later Felix returned with his wife Drusilla, who was Jewish. He sent for Paul and listened to him speak about trusting in Christ Jesus.
Bayan wadansu kwanaki, Filikus da mai dakinsa Druskila, ita Bayahudiya ce, ya kuma aika a kira Bulus ya saurare shi game da bangaskiya cikin Kristi Yesu.
25 He discussed with them about living right, self-control, and the coming judgment. Felix became alarmed and told Paul, “You can go now, and I'll send for you when I get the chance.”
Amma sa'adda Bulus yake bayyana zancen adalci, kamunkai, da hukunci mai zuwa, Filikus ya firgita ya ce, “Yanzu ka tafi. Amma idan na sami zarafi an jima, zan sake neman ka.”
26 Hoping that Paul would give him a bribe, Felix often sent for Paul and talked with him.
A wannan lokacin, yasa zuciya Bulus zai bashi kudi, yayi ta nemansa akai-akai domin yayi magana da shi.
27 Two years passed and Felix was succeeded by Porcius Festus. To stay in favor with the Jews, Felix left Paul in prison.
Bayan shekaru biyu, Borkiyas Festas ya zama gwamna bayan Filikus, domin neman farin jini a wurin Yahudawa, ya ci gaba da tsaron Bulus a gidan yari.

< Acts 24 >