< Acts 16 >

1 Paul went first to Derbe, and then on to Lystra, where he met a believer by the name of Timothy. He was the son of a Jewish Christian mother, and his father was Greek.
Bulus ya kuma isa Darbe da Listira, in da akwai wani almajiri mai suna Timoti a wurin, dan wata Bayahudiya wadda ta ba da gaskiya; ubansa kuwa Baheline ne.
2 The brothers at Lystra and Iconium spoke well of him.
Ana maganar kirki a kansa ta bakin 'yan'uwa da ke Listira da Ikoniyan.
3 Paul wanted Timothy to travel with him, so he circumcised him because the Jews in the area all knew that Timothy's father was Greek.
Bulus ya yi wa Timoti kaciya, domin yana so su yi tafiya tare, domin kuma saboda Yahudawan da ke wurin, sun san cewa ubansa Baheline ne.
4 As they went through the different towns they gave them the requirements the apostles and elders in Jerusalem had said should be observed.
Suna shiga cikin biranen, suna yi wa iklisiyoyi gargadi da su yi biyayya da umurnan da Manzanni da dattawa suka rubuta a Urushalima.
5 The churches were strengthened in their trust in the Lord and every day their numbers increased.
Bangaskiyar iklisiyoyi kuwa ta karu, ana kuma samun karuwa na wadanda suke ba da gaskiya kowace rana.
6 They traveled through the districts of Phrygia and Galatia, since the Holy Spirit prevented them from going to the province of Asia to speak the word.
Bulus da abokan aikin sa sun shiga cikin lardin Firigiya da Galatiya, tun da Ruhu Mai Tsarki ya hana su wa'azin kalmar a cikin yankin Asiya.
7 When they arrived at the border of Mysia they tried to enter Bithynia, but the Spirit of Jesus would not allow them to enter.
Sun zo kusa da Misiya, da nufin shiga cikin Bitiniya, Ruhun Yesu ya hana su.
8 So they passed by Mysia and went down to Troas.
Da suka ratse ta cikin Misiya, sai suka shiga birnin Taruwasa.
9 There Paul saw in vision during the night a man from Macedonia standing up, pleading with him, “Please come over to Macedonia and help us!”
Bulus ya ga wahayi cikin dare, wani mutumin Makidoniya na kiransa, yana cewa. ''Ka zo Makidoniya ka taimake mu''.
10 After Paul saw this vision, we immediately made arrangements to go to Macedonia, since we concluded that God had called us to share the good news with them.
Bulus, da ganin haka, ya kama hanya zuwa Makidoniya, da tunanin Allah ne ya ke so su kai wa mutanen Makidoniya bishara.
11 We set sail from Troas and made straight for Samothrace. The next day we went on to Neapolis,
Da barin Taruwasa, Bulus da kungiyarsa sun shiga jirgin ruwa zuwa Samutaraki, da gari ya waye kuma sun tafi Niyafolis;
12 and from there to Philippi, the most important town in Macedonia, and also a Roman colony. We stayed in this city for several days.
Daga nan kuma suka tafi Filibi, birni na Makidoniya, mai muhimmanci ne a yankin Roma, in da mun yi zango kwanaki da dama.
13 On the Sabbath day we went out of the town gates down to the riverside where we thought people would come to pray. We sat down and talked with the women that had gathered there.
Ranar Asabaci mun je kofar gari, gefen rafi, da tunanin samun wurin addu'a. Mun zauna mun kuma yi magana da matan da sun taru a wurin.
14 One of them was called Lydia, who sold purple cloth from the town of Thyatira. She worshiped God, and she listened to us. The Lord opened her mind to what Paul was saying, and she accepted what he told her.
Wata mace mai suna Lidiya, 'yar kasuwa ce a birnin Tiyatira, mai bautar Allah ce, ta saurare mu. Ubangiji ya bude zuciyarta, ta mai da hankali ga maganar da Bulus ke fadi.
15 After she and all her household were baptized, she pleaded with us, “If you really think that I'm truly committed to the Lord, then come and stay at my house.” She kept on insisting until we agreed!
Sa'anda da aka yi mata Baftisma tare da mutanen gidanta, ta ce da mu, “Idan kun dauke ni mai bautar Allah, ku zo gidana ku zauna.” Sai ta rinjaye mu.
16 One day when we were going down to the place of prayer we met a slave girl possessed by an evil spirit. She earned her masters a great deal of money by fortune-telling.
A daidai wannan lokaci, muna tafiya wurin addu'a, wata yarinya mai ruhun duba ta hadu da mu. Iyayen gijinta na arziki da ita sosai.
17 This girl followed Paul and the rest of us around, shouting, “These men are the servants of Almighty God. They are telling you how to be saved!”
Tana bin Bulus, tare da mu, tana fadi da murya mai karfi cewa, ''Wadannan mutanen, bayin Allah mafi daukaka ne, suna sanar maku hanyar ceto ne''.
18 She went on doing this for several days. This bothered Paul so he turned around and told the spirit, “I command you in the name of Jesus Christ to leave her!” The spirit immediately left her.
Ta dauki kwanaki tana haka. Amma Bulus ya yi fushi da ita ainun, ya juya ya umarci ruhun, ya ce, ''Na umarce ka, ka rabu da ita a cikin sunan Yesu Almasihu''. Ruhun ya yi biyayya ya rabu da ita nan take.
19 But when her masters saw they had lost their means of making money, they grabbed hold of Paul and Silas and dragged them before the authorities at the marketplace.
Da iyayengijinta suka ga cewa hanyar shigar kudinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila, suka ja su cikin kasuwa suka kai su gaban mahunkunta.
20 They brought them in front of the magistrates, and accused them: “These Jewish men are causing a great disturbance in our town,” they said.
Da suka kai su Kotu, suka ce, ''Wadannan mutane Yahudawa ne, suna kawo tashin hankali a birninmu.
21 “They're advocating things that are illegal for us as Romans to accept or to practice.”
Suna koyar da abubuwa da ba su karbuwa a gare mu, balle mu aikata, a matsayinmu na Romawa.”
22 The crowd joined together in an attack on them. The magistrates tore off Paul and Silas' clothes, and ordered them beaten with rods.
Sai jama'a gaba daya sun tayar wa Bulus da Sila; alkalan kuma sun yage rigunansu, sun ba da umarni a duki Bulus da Sila da bulala.
23 After giving them a severe beating, they threw them into prison, ordering the jailer to keep them locked up.
Bayan dukan, an jefa su Bulus a kurkuku, an ba mai tsaron kurkukun umurni ya kulle su da kyau, kada su gudu.
24 The jailer followed his orders. He threw Paul and Silas into the inner cell and shackled their feet in the stocks.
Shi kuma ya yi hakanan, ya sa masu sarkoki a kafafun su, kamar yadda aka umurce shi.
25 Around midnight Paul and Silas were praying and singing praises to God, and the other prisoners were listening to them.
Da tsakar dare, Bulus da Sila suna yin adu'a, su na raira wakoki ga Allah, sauran 'yan sarkar su na jin su.
26 Suddenly a tremendous earthquake shook the foundations of the prison. Immediately all the doors flew open and everyone's chains fell off.
Nan da nan sai ga wata girgizar kasa, wadda ta sa ginshikan kurkukun sun kadu, nan da nan kofofin kurkukun sun bude, 'yan sarka kuma, sarkokin su sun karkatse.
27 The jailer woke up and saw the doors of the prison wide open. He drew his sword and was about to kill himself, thinking that the prisoners had escaped.
Mai tsaron kurkukun ya tashi daga barci ya ga kofofin kurkukun a bude, ya zaro takobi, zai kashe kan sa, a tunanin sa, 'yan sarkar sun gudu.
28 But Paul shouted out, “Don't hurt yourself—we're all still here!”
Amma Bulus ya ta da murya da karfi, ya ce, ''kada kayi wa kanka barna, domin dukan mu muna nan''.
29 The jailer asked for lights to be brought and rushed in. Shaking with fear he fell down before Paul and Silas.
Mai tsaron kurkukun ya aika a kawo fitila, ya shiga ciki a gurguje da rawan jiki, ya fadi a gaban Bulus da Sila,
30 He escorted them out and asked them, “Sirs, what do I have to do so I can be saved?”
ya fitar da su waje ya ce, ''Shugabanni, me ya kamata in yi domin in tsira?''
31 “Trust in the Lord Jesus, and you will be saved—you and your whole household,” they replied.
Sun ce masa, ''ka ba da gaskiya ga Yesu Ubangiji, da kai da gidan ka, za ku sami tsira''.
32 Then they shared the word of the Lord with him and everyone who lived in his house.
Bulus da Sila suka fada masa maganar Ubangiji, tare da iyalinsa.
33 Even though it was late at night he bathed their wounds, and he was baptized right away, along with all his family.
Shi mai tsaron kurkukun ya dauke su cikin daren, ya wanke raunukansu, an kuma yi masa Baftisma nan da nan tare da iyalinsa.
34 He took them home and had a meal prepared for them. The jailer and his whole family were full of joy because they trusted in God.
Ya kai Bulus da Sila gidansa, ya ba su abinci. Murna ta cika gidan mai tsaron kurkukun, domin iyalin sa duka sun ba da gaskiya ga Allah.
35 Early the next day the magistrate sent officials to the jailer, telling him, “Release those men.”
Da gari ya waye, alkalai sun ba da sako a saki Bulus da Sila.
36 The jailer told Paul, “The magistrates have sent word to release you. So you can leave, and go in peace.”
Mai tsaron kurkukun kuwa ya sanar wa Bulus wannan magana ta alkalan, saboda haka ya ce wa Bulus, ''Ku tafi cikin salama''.
37 But Paul told them, “They publicly beat us without a trial—and yet we're Roman citizens! Then they threw us in prison. Now they want to quietly let us go? No, they should come themselves and release us!”
Amma Bulus ya ce masu, “Sun yi mana duka a fili a gaban mutane mu da muke Romawa, ba a kashe mu ba, sun kuma sa mu a kurkuku; suna koran mu a asirce? Su zo da kansu su fitar da mu.
38 The officials went back and reported this to the magistrates. When they heard that Paul and Silas were Roman citizens they were really worried,
Masu tsaron kurkuku sun mayar da maganar Bulus ga alkalan, wanda ya sa sun firgita, da jin cewa Bulus da Sila Romawa ne.
39 and went to apologize to them. They escorted them out and begged them to leave town.
Alkalai da kansu sun zo sun roki Bulus da Sila; da suka fitar da su daga kurkukun, sun ce wa Bulus da Sila su bar birnin.
40 So Paul and Silas left the prison and went to Lydia's house. There they met with the believers, encouraged them, and then went on their way.
Da hakanan ne Bulus da Sila suka fita daga kurkuku, sun je gidan Lidiya. Da Bulus da Sila sun ga 'yan'uwa, sun karfafa su, sa'annan suka bar birnin.

< Acts 16 >