< 2 Thessalonians 1 >
1 This letter comes from Paul, Silvanus, and Timothy to the church of the Thessalonians who belong to God our Father and the Lord Jesus Christ.
Bulus da Silbanus da Timoti, zuwa ga ikilisiyar Tasolonika cikin Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu.
2 May you have grace and peace from God the Father and the Lord Jesus Christ.
Bari alheri ya kasance tare da ku da salama daga Allah Ubanmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.
3 We keep on thanking God for you, brothers and sisters—we just have to! This is the right thing to do because your trust in God is growing in leaps and bounds, and the love you all have for each other increases more and more.
Lallai ne mu godewa Allah kulluyaumin domin ku, yan'uwa. Domin hakan dai dai ne, saboda bangaskiyarku ta karu sosai, kuma kaunar junanku tana karuwa.
4 We speak so proudly of you among the churches of God because of your patient courage and trust in God during all the persecution and trouble you're going through.
Mu da kanmu muna fahariya da ku a ikilisiyoyin Allah. Muna maganar hakurinku da bangaskiyarku a cikin dukkan tsananin da kuke fuskanta. Muna maganar kuncin da kuke jimrewa.
5 For this is evidence that God is right in the decisions he makes, and that you deserve the kingdom of God for which you are suffering.
Wannan itace alamar shari'ar Allah ta adalci. Sakamakon haka shine za a dauke ku cancantattu na mulkin Allah wanda kuke wahala dominsa.
6 Since God does what's right he will deal appropriately with those who cause you trouble.
Adalci ne ga Allah ya mayar da kunci ga wadanda suke kuntata maku,
7 He will free you from your suffering—and us too—when the Lord Jesus appears from heaven in blazing fire with his powerful angels,
ya kuma baku hutu ku dake shan wuya tare da mu. Zai yi haka ne a bayyanar Ubangiji Yesu daga sama da Mala'ikun ikonsa.
8 bringing judgment on those who reject God and refuse to accept the good news of our Lord Jesus.
A cikin wuta mai huruwa zai dau fansa bisa wadanda basu san Allah ba da wadanda basu karbi bisharar Ubangijinmu Yesu almasihu ba.
9 They will rightly experience the consequence of eternal loss, separated from the presence of the Lord and his glorious power, (aiōnios )
Za su sha azaba ta hallaka har abada daga fuskar Ubangiji da kuma daukakar ikonsa. (aiōnios )
10 on the day when he comes to receive glory from his people, admired by all those who trust in him. This includes you because you were convinced about what we told you.
Zai yi wannan lokacin da yazo a wannan rana don jama'arsa su daukaka shi, kuma ya zama abin mamaki ga dukkan wadanda suka bada gaskiya. Domin kun gaskata shaidarmu a gare ku.
11 That's why we continue to pray for you, that our God may make you worthy of what he's called us to do. May God powerfully fulfill every desire you have to do good and every action that comes from trusting him
Saboda wannan muke addu'a kullum domin ku. Muna addu'a domin Allahnmu ya sa ku cancanci kiran ku. Muna addu'a ya biya ku muradin ku na yin nagarta da dukkan wani aikin bangaskiya da kuma iko.
12 so that the name of our Lord Jesus may be honored by what you do—and in turn you are honored by him through the grace of our God and the Lord Jesus Christ.
Muna addu'a haka domin sunan Ubangijinmu Yesu ya sami daukaka daga gare ku. Addu'armu itace ya daukaka ku, saboda alherin Allahnmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.