< 2 Samuel 4 >

1 When Ishbosheth, son of Saul, heard that Abner had died in Hebron, he was very discouraged, and everyone in Israel was shocked.
Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
2 Ishbosheth had two commanders of his raiding bands, brothers by the name of Baanah and Rechab. They were the sons of Rimmon of the tribe of Benjamin from the town of Beeroth. Beeroth is considered part of the territory of Benjamin,
To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
3 because the people who had lived in Beeroth before ran away to Gittaim and lived there as foreigners right up to the present.
domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
4 Jonathan, son of Saul, had a son lame in both feet. He was five years old when the news about the deaths of Saul and Jonathan had come from Jezreel. His nurse had picked him up and ran away, but as she rushed to get away, he fell and became lame. His name was Mephibosheth.
(Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
5 Rechab and Baanah, sons of Rimmon from Beeroth, went to Ishbosheth's house, arriving in the heat of the day as the king was taking his midday rest.
To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
6 The woman doorkeeper had been cleaning wheat, but she had grown tired and fallen asleep, so Rechab and Baanah were able to slip inside.
Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
7 They had gone into the house while Ishbosheth was asleep on his bed in his bedroom. After stabbing and killing him, they cut off his head which they took with them, and they traveled all night by the Jordan Valley road.
Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
8 They took the head of Ishbosheth to David in Hebron. They told the king, “Here is the head of Ishbosheth, son of Saul, your enemy who tried to kill you. Today the Lord has taken revenge on Saul and his family for my lord the king.”
Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
9 But David answered Rechab and his brother Baanah, sons of Rimmon from Beeroth, “As the Lord lives, who has saved me from all my troubles,
Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
10 when someone told me, ‘Look, Saul is dead’ and he thought he was bringing me good news, I grabbed him and had him put him to death at Ziklag. That was what he got for bringing me his news!
sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
11 Even more so then, when evil men kill a good man in his own house, and in his own bed, shouldn't I demand you pay for his life with your own lives, and exterminate you!”
Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
12 David gave the order to his men, and they killed Rechab and Baanah. They chopped off their hands and feet, and hung their bodies by the pool in Hebron. Then they took Ishbosheth's head and buried it in Abner's grave in Hebron.
Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.

< 2 Samuel 4 >