< 2 Samuel 21 >
1 Once during David's reign there was a famine for three years in a row, and David asked the Lord about it. The Lord replied, “It's because Saul and his family are guilty of murdering the Gibeonites.”
Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
2 David summoned the Gibeonites and spoke with them. The Gibeonites were not Israelites, but what was left of the Amorites. The Israelites had sworn an oath to them, but in his nationalistic passion for the Israelites and Judah, Saul had tried to wipe them out.
Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
3 “What can I do for you?” David asked the Gibeonites. “How can I compensate you so that you may bless the Lord's people?”
Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
4 “This isn't a question of us receiving payment in silver or gold from Saul or his family,” the Gibeonites replied. “In addition we don't have the right to have anyone in Israel put to death for us.” “I'll do whatever you ask,” David answered.
Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
5 They replied, “Regarding the man who destroyed us, who planned to prevent us having any place to live in the whole country of Israel,
Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
6 have seven of Saul's male descendants be handed over to us, and we will hang them in the presence of the Lord at Gibeon of Saul, the Lord's chosen one.” “I will hand them over to you,” said the king.
a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
7 However, the king spared Mephibosheth, son of Jonathan, son of Saul, because of the oath sworn before the Lord between David and Jonathan, son of Saul.
Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
8 The king took Armoni and Mephibosheth, the two sons of Rizpah the daughter of Aiah, whom she had borne to Saul, and the five sons of Merab, the daughter of Saul, whom she had borne to Adriel, son of Barzillai the Meholathite.
Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
9 He handed them over to the Gibeonites, and they hanged them on the hill in the presence of the Lord. All seven of them died at the same time, executed at the beginning of the barley harvest.
Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
10 Rizpah the daughter of Aiah took some sackcloth and spread it out for herself on a rock. From the beginning of the harvest until the time the rains came and poured down on the bodies, she kept the birds away from them during the day and the wild animals at night.
Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
11 When David heard what Rizpah the daughter of Aiah, Saul's concubine of Saul had done,
Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
12 he retrieved the bones of Saul and his son Jonathan from the men of Jabesh-gilead, who had taken them from the public square of Beth-shan where the Philistines had hung the bodies after they had killed Saul at Gilboa.
sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
13 David had the bones of Saul and his son Jonathan brought back, and also had the bones of those who had been hanged gathered up.
Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
14 They buried the bones of Saul and his son Jonathan at Zela in the land of Benjamin, in the tomb of Saul's father Kish. Once they finished doing everything the king had ordered, God answered their prayers to end the famine in the land.
Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
15 There was war once more between the Philistines and Israel. David went down with his men to fight the Philistines, and he got worn out.
Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
16 Ishbi-benob, one of the descendants of Rapha, whose bronze spear weighed three hundred shekels, and who was carrying a new sword, said he was going to kill David.
Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
17 But Abishai, son of Zeruiah, came to his rescue, attacked the Philistine, and killed him. Then David's men swore to him, “Don't ever go out with us to battle again, so that the Israel's light isn't snuffed out!”
Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
18 Some time after this there was another battle with the Philistines at Gob. But then Sibbecai the Hushathite killed Saph, one of the descendants of Repha.
Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
19 In another battle with the Philistines at Gob, Elhanan, son of Jair, from Bethlehem, killed the brother of Goliath the Gittite. The shaft of his spear was as thick as a weaver's rod.
Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
20 In yet another battle at Gath, there was a gigantic man, who had six fingers on each hand and six toes on each foot, making twenty-four all. He too was descended from the giants.
Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
21 But when he insulted Israel, Jonathan, son of Shimea, David's brother, killed him.
Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
22 These four were the descendants of the giants in Gath, but they were all killed by David and his men.
Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.