< 2 Peter 2 >
1 But just as there were false prophets among the people then, there will be false teachers among you. They subtly introduce false and destructive teachings, even denying the Lord who redeemed them, quickly bringing destruction on themselves.
Amma a dā akwai annabawan ƙarya a cikin mutane, kamar yadda za a sami malaman ƙarya a cikinku. A ɓoye za su shigar da karkataccen koyarwa mai hallaka, har ma su yi mūsun Ubangiji mai iko duka wanda ya saye su suna kawo wa kansu hallaka farat ɗaya.
2 Many will follow their immoral perversions, and because of them people will condemn the way of truth.
Da yawa za su bi hanyoyinsu na rashin kunya su kuma sa a rena hanyar gaskiya.
3 They will greedily exploit you with false tales. However, they are already condemned: their sentence has been hanging over them for a long time, their destruction won't be postponed.
Cikin kwaɗayinsu waɗannan malaman ƙarya za su cuce ku da tatsuniyoyin da suka ƙaga. Hukuncinsu yana a rataye a kansu tun da daɗewa, hallakarsu kuma ba ta barci.
4 For God didn't even spare the angels when they sinned. He threw them into Tartarus, holding them in dark pits ready for judgment. (Tartaroō )
Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō )
5 God didn't spare the ancient world either, but he protected Noah who told people about the God who did right. He was one of the eight who were saved when God sent a flood upon a world of evil people.
in har bai ƙyale duniya ta dā ba sa’ad da ya kawo ambaliya a kan mutanenta marasa tsoron Allah, amma ya kiyaye Nuhu, mai wa’azin adalci, da kuma waɗansu bakwai;
6 God condemned the cities of Sodom and Gomorrah to total destruction, burning them to ash, as an example of what will happen to those who live evil lives.
in har ya hukunta biranen Sodom da Gomorra ta wurin ƙone su suka zama toka, ya kuma maishe su misali na abin da zai faru da marasa tsoron Allah;
7 But God rescued Lot because he was a good man, sickened by the disgusting immorality of his neighbors.
in kuwa har ya ceci Lot, mai adalci, wanda ya damu ainun da ƙazamar rayuwar mutane marasa bin doka;
8 (Lot lived among them, but he did what was good and right. He saw and heard what they did day after day, and their wickedness tormented him.)
(adon kuwa abin da adalin nan ya yi, ya kuma gani, sa’ad da yake a cikinsu, sai kowace rana yakan ji ciwon aikinsu na kangara a zuciyarsa mai adalci)
9 As you can see, the Lord is able to rescue from their troubles those who respect him, and to keep the wicked until the day of judgment when their punishment is completed.
in haka ne, to, Ubangiji ya san yadda zai ceci mutane masu tsoron Allah daga gwaje-gwaje, yă kuma tsare marasa adalci don ranar hukunci, har yă zuwa ranar shari’a.
10 This is especially so for those who follow their corrupt human desires, and contemptuously disregard authority. Arrogant and proud, they're not even afraid to defame heavenly beings.
Wannan gaskiya ce musamman ga waɗanda suke bin sha’awace-sha’awacen lalaci na mutuntaka, suna kuma rena masu mulki. Da ƙarfin hali da kuma girman kai, waɗannan mutane ba sa tsoro kawo zargin ɓata sunan talikan sama;
11 Angels, on the other hand, even though they are stronger and more powerful, don't disparage them before the Lord.
duk da haka ko mala’iku ma da suka fi su ƙarfi suka kuma fi su iko, ba sa kawo irin wannan zargi na ɓata suna game da waɗannan talikai a gaban Ubangiji.
12 These people are like mindless beasts, produced like farm animals to be captured and slaughtered. They condemn things they don't know anything about, and just like animals they will be destroyed.
Amma waɗannan mutane suna yin saɓo a kan abubuwan da ba su fahimta ba. Suna kama da dabbobi marasa hankali, halittun da suke bin abin da jikinsu ya faɗa musu kawai, waɗanda aka haifa don a kama a hallaka, kuma kamar dabbobi su ma za su hallaka.
13 They will be paid back in harm for the harm they have done. Their idea of fun is to commit their evil lusts in broad daylight. They are stains and blemishes on your community. They enjoy their deceptive pleasures even while they eat together with you.
Za a yi musu sakamako da muguntar da suka yi. A ra’ayinsu jin daɗi shi ne a yi annashuwa da rana tsaka. Su ƙazamai ne marasa kunya, suna cike da jin daɗin sha’awace-sha’awacensu yayinda suke cin biki tare da ku.
14 They're always on the lookout for adulterous relationships—they just can't stop sinning. They seduce the vulnerable; they have trained themselves in greed; they are offspring under a curse.
Idanunsu sun cike da zina, ba sa ƙoshi da yin zunubi; suna jarrabtar waɗanda ba tsayayyu ba; gwanaye ne a kan kwaɗayi, la’anannun iri!
15 They have abandoned the right path and went astray, following the way of Balaam, the son of Beor, who loved to be paid for doing evil.
Sun bar miƙaƙƙiyar hanya suka bauɗe suna bin hanyar Bala’am ɗan Beyor, wanda ya yi ƙaunar hakkin mugunta.
16 But he was told off for his evil actions—a dumb donkey spoke with a human voice and stopped the prophet's foolishness!
Amma an tsawata masa saboda laifinsa ta wurin jaki, dabbar da ba ta magana, wadda ta yi magana da muryar mutum ta kuma kwaɓi haukan annabin.
17 People like these are springs without water, mists blown away by the wind. They are destined for blackest darkness—forever. ()
Waɗannan mutane maɓulɓulai ne babu ruwa da kuma hazon da guguwar iska take kora. An shirya matsanancin duhu dominsu.
18 Inflated with their own nonsense, they appeal to sensual desires, luring back into immorality those who have only just escaped from those who live in error.
Gama suna surutai banza na girman kai, ta wurin son bin fasikanci na mutuntaka, sukan jan hankulan mutanen da suke kuɓucewa daga waɗancan masu zama cikin kuskure.
19 They promise them freedom, even though they themselves are slaves to depravity. “You are a slave to whatever conquers you.”
Suna yin musu alkawarin’yanci, yayinda su kansu bayi ne ga aikin lalata gama mutum bawa ne ga duk abin da ya mallake shi.
20 If people manage to escape from the evil influence of the world by knowing the Lord and Savior Jesus Christ, and then get tangled up in sin again and are defeated, they are worse off than they were in the first place.
In har sun kuɓuta daga lalacin duniya ta wurin sanin Ubangijinmu da kuma Mai Cetonmu Yesu Kiristi sai suka sāke koma a cikin lalacin, har ya rinjaye su, za su fi muni a ƙarshe fiye da farko.
21 It would have been better not to have known the right way of truth, than to have known it and then turn away from the sacred instructions they'd been given.
Zai fi musu kyau da ba su taɓa sanin hanyar adalci ba, fiye da a ce sun sani sa’an nan su juya bayansu ga umarni mai tsarkin nan da aka ba su.
22 This proverb has come true for them: “The dog has returned to its own vomit, and the washed pig has gone back to rolling in the mud.”
A kansu karin maganan nan gaskiya ce, “Kare ya koma kan amansa,” da kuma, “Alade da aka yi wa wanka, ya koma birgimarsa cikin laka.”