< 1 Samuel 8 >
1 When Samuel grew old, he made his sons leaders over Israel.
Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
2 His first son was named Joel, and his second son was named Abijah. They were rulers in Beersheba.
Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
3 However, his sons did not follow his ways. They were corrupt, making money by accepting bribes and perverting justice.
Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
4 So the elders of Israel all joined together and came to meet Samuel at Ramah.
Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
5 “Look here,” they told him, “you are old, and your sons do not follow your ways. Choose a king to rule over us like all the other nations.”
Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
6 Samuel thought this was a bad idea when they said, “Give us a king to rule over us,” so he prayed to the Lord about it.
Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
7 “Do what the people tell you,” the Lord said to Samuel, “because it's not you they're rejecting, but me as their king.
Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
8 They're doing just as they have always done since I led them out of Egypt right up to now. They have abandoned me and worshiped other gods, and they're doing just the same to you.
Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
9 So do what they want, but give them a solemn warning—explain to them what a king will do when he rules over them.”
Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
10 Samuel repeated all that the Lord had said to the people asking him to give them a king.
Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
11 “This is what a king will do when he rules over you,” he told them. “He will take your sons and make them serve as charioteers and horsemen, and to run as a guard in front of his chariot.
Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
12 Some of them he will make commanders of thousands and commanders of fifties, and some will have to plow his fields and reap his harvest. Some will be assigned to making weapons of war and chariot equipment.
Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
13 He will take your daughters and have them work as perfume-makers, cooks, and bakers.
Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
14 He will take your best fields, vineyards, and olive groves and give them to his officials.
Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
15 He will take a tenth of your grain harvest and the produce of your vineyards and allocate it to his chief officers and officials.
Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
16 He will take your male servants and your female servants, and your best young men and your donkeys, and make them work for him.
Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
17 He will take a tenth of your flocks, and you yourselves will be his slaves.
Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
18 On that day you will plead to be rescued from the king you have chosen, but the Lord won't answer you then.”
Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
19 But the people refused to listen to what Samuel said. “No!” they insisted. “We want our own king!
Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
20 That way we can be like all the other nations. Our king will rule us, and will lead us when we go out to fight our battles.”
Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
21 Samuel listened to everything the people said and repeated it to the Lord.
Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
22 The Lord told Samuel, “Do what they say and give them a king.” Then Samuel told the Israelites, “Go back to your homes.”
Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”