< 1 Chronicles 11 >

1 All the Israelites gathered to meet with David in Hebron. They told him, “We are your flesh and blood.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 In recent times, even though Saul was king, you were the real leader of Israel. The Lord your God told you, ‘You will be the shepherd of my people, and you will be the leader of my people Israel.’”
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 All the elders of Israel came to the king at Hebron, and David made a solemn agreement with them before the Lord. There they anointed David as king of Israel, as the Lord had promised through Samuel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 Then David and all the Israelites went to Jerusalem (formerly known as Jebus) where the Jebusites lived.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 The Jebusites told David, “You will not enter here!” But David did capture the fortress of Zion, now known as the City of David.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 David had said, “Whoever is first to attack the Jebusites will be my commander-in-chief.” Since Joab, son of Zeruiah, was the first, he became commander-in-chief.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 David decided to love in the fortress, which is why they named it after him the City of David.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 He built up the city all around it, from the Millo in a circuit all around, while Joab repaired the rest of the city.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 David became more and more powerful, for the Lord Almighty was with him.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 These were the leaders of David's powerful warriors who, along with all the Israelites, gave him strong support in becoming king, just as the Lord had promised would happen to Israel.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 This is the list of the leading warriors who supported David: Jashobeam, son of Hachmoni, leader of the Three. Using his spear, he once killed 300 men in a single battle.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 After him came Eleazar, son of Dodo the Ahohite, one of the Three leading warriors.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 He was with David at Pas-dammin when the Philistines gathered for battle that took place in a field full of barley. The Israelite army ran away when the Philistines attacked,
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 but David and Eleazar took a stand in the middle of the field, defending their ground and killing the Philistines. The Lord saved them by giving them a great victory.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 Another time, the Three, who were part of the Thirty leading warriors, went down to meet David when he was at the cave of Adullam. The Philistine army was camped in the valley of Rephaim.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 At the time David was in the stronghold, and the Philistine garrison was in Bethlehem.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 David was feeling really thirsty, and he said, “If only someone could bring me a drink of water from the well beside the entrance gate to Bethlehem!”
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 The Three broke through the Philistine defenses, took some water from the well at Bethelehem's gate, and brought it back to David. But David refused to drink it, and poured it out as an offering to the Lord.
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 “God forbid that I should do this!” he said. “It would be like drinking the blood of these men who risked their lives! They risked their lives to bring me a drink.” So he did not drink it. This is just some of the things the Three leading warriors did.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 Abishai, Joab's brother, was leader of the second Three. Using his spear, he once killed 300 men, and became famous among the Three.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 He was the most highly regarded of the Three and was their commander, though he was not one of the first Three.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Benaiah, son of Jehoiada, a strong warrior from Kabzeel, did many amazing things. He killed two sons of Ariel of Moab. He also went after a lion into a pit in the snow and killed it.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 Another time he killed an Egyptian—a huge man who stood seven foot six inches tall. The Egyptian had a spear whose shaft was as thick as a weaver's rod. Benaiah attacked him with just a club, but he was able to grab the spear from the Egyptian's hand, and killed him with his own spear.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 These were the kind of things Benaiah did that made him as famous as the Three leading warriors.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 He was the most highly regarded of the Thirty, though he was not one of the Three. David put him in charge of his personal bodyguard.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 Other leading warriors were: Asahel, Joab's brother; Elhanan, son of Dodo, from Bethlehem;
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Shammoth the Harorite; Helez the Pelonite;
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Ira, son of Ikkesh from Tekoa; Abiezer from Anathoth;
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sibbecai the Hushathite; Ilai the Ahohite;
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharai of Netophah; Heled, son of Baanah of Netophah;
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Ithai, son of Ribai from Gibeah of the Benjamites; Benaiah the Pirathonite;
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Hurai from the valleys of Gaash; Abiel the Arbathite;
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Azmaveth the Baharumite; Eliahba the Shaalbonite;
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 the sons of Hashem the Gizonite; Jonathan, son of Shagee the Hararite;
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Ahiam, son of Sachar the Hararite; Eliphal, son of Ur;
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Hepher the Mecherathite; Ahijah the Pelonite;
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hezro the Carmelite; Naarai, son of Ezbai;
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Joel the Nathan's brother; Mibhar, son of Hagri;
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Zelek the Ammonite; Naharai the Beerothite; Joab's armor-bearer, son of Zeruiah;
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Ira the Ithrite; Gareb the Ithrite;
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Uriah the Hittite; Zabad son of Ahlai;
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Adina, son of Shiza the Reubenite, leader of the Reubenites, and the thirty who were with him;
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan, son of Maacah; Joshaphat the Mithnite;
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Uzzia the Ashterathite; Shama and Jeiel, the sons of Hotham the Aroerite;
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Jediael, son of Shimri, and his brother, Joha the Tizite;
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliel the Mahavite; Jeribai and Joshaviah, the sons of Elnaam; Ithmah the Moabite;
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliel; Obed; and Jaasiel the Mezobaite.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.

< 1 Chronicles 11 >