< Mark 2 >

1 Well a few days later, He again entered Capernaum, and it was heard that He was at home.
Da ya dawo Kafarnahum bayan yan kwanaki kadan, aka ji cewa yana gida.
2 Without delay so many were gathered together that there was no more room, not even around the door, and He was speaking the Word to them.
Da yawa suka taru a can, ba wuri har kofa, sai Yesu ya yi masu magana.
3 Then four men came, carrying a paralytic to Him.
Sai wadansu mutane su ka zo wurinsa dauke da wuni mutum shanyayye, mutane hudu na dauke da shi.
4 And not being able to get near Him because of the crowd, they removed the roof where He was; upon breaking through they lowered the pallet on which the paralytic was lying.
Lokacin da ba su iya zuwa kusa da shi ba domin yawan jama'a, sai su ka daye jinkar dakin daidai da inda ya ke. Bayan da suka huda ramin suka saukar da gado wanda shanyayyen ke kwance a kai.
5 So seeing their faith Jesus says to the paralytic, “Son, your sins are forgiven you.”
Da ganin bangaskiyarsu, Yesu ya ce wa shanyayyen mutumin, “Da, an gafarta maka zunuban ka”.
6 Now some of the scribes were sitting there, and reasoning in their hearts:
Amma wadansu marubuta da ke zaune a nan, suka yi tunani aransu.
7 “Why does this guy speak blasphemies like that? Who can forgive sins but God alone?”
Yaya wannan mutum zai yi magana haka? Ya yi sabo! wa ke iya gafarta zunubi “sai Allah kadai?”
8 Immediately Jesus perceived in His spirit what they were reasoning within themselves and said to them: “Why are you reasoning these things in your hearts?
Nan da nan Yesu ya sani a ruhunsa, abinda suke tunani a tsakaninsu. Ya ce masu, “Me ya sa kuke tunanin wannan a zuciyarku?
9 Which is easier: to say to the paralytic, ‘Your sins have been forgiven’, or to say, ‘Get up, pick up your pallet and start walking!’?
Me yafi sauki a cewa shanyayyen mutumin, 'An gafarta maka zunuban ka' ko kwa a ce masa, 'tashi, ka dauki shinfidarka, ka yi tafiyarka'?
10 But so that you may know that the Son of the Man has authority on the earth to forgive sins”—He says to the paralytic:
Amma domin ku san cewa Dan mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya, ya ce wa shanyayyen,
11 “To you I say, get up, pick up your pallet and go to your house!”
''Na ce maka, tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidan ka.”
12 So forthwith he got up, picked up his pallet and went out in front of them all; so that all were amazed and glorified God, saying, “We never saw anything like this!”
Sai nan da nan ya tashi ya dauki tabarmarsa, ya fita gidan a gabansu, dukansu su ka yi mamaki, su ka girmama Allah, ''suka ce ba mu taba ganin abu irin wannan ba.”
13 Then He went out again by the sea; and the whole crowd came to Him, and He began to teach them.
Ya sake fita gefen tafki, dukan taron jama'a suka zo wurinsa, sai ya koya masu.
14 As He passed by, He saw Levi the son of Alphaeus sitting at the tax office, and He said to him, “Follow me!” So he got up and followed Him.
Sa'adda ya na wucewa, ya ga Levi dan Halfa yana zaune a wurin karbar haraji, sai ya ce masa, “Ka biyo ni.” Ya tashi, ya bi shi.
15 Now it happened, as He was reclining at the table in his house, that many tax collectors and sinners joined Jesus and His disciples at the table; for there were many and they followed Him.
Sa'adda Yesu ya shiga gidan Levi yana cin abinci, masu karbar haraji da masu zunubi da yawa su ka zo wurinsa da almajiransa, jama'a masu yawan gaske suka ka bi shi.
16 The scribes and the Pharisees, seeing Him eating with the tax collectors and sinners, said to His disciples, “Why is it that He is eating and drinking with the tax collectors and sinners?”
Da Marubuta wadanda su ke Farisawa, sun ga cewa Yesu na cin abinci da masu zunubi da masu karbar haraji, sai su ka ce wa almajiransa, “Me ya sa ya ke ci da masu karbar haraji da mutane masu zunubi?”
17 Upon hearing it Jesus said to them: “It is not the healthy who have need of a doctor, but those who are sick. I did not come to call the righteous, but sinners to repentance.”
Da Yesu ya ji wannan ya ce masu, “Mutane wadanda ke da lafiya a jiki ba su bukatar likita; sai dai ko marasa lafiya ke bukatarsa. Ban zo domin in kira mutane masu a dalci ba, amma mutane masu zunubi.”
18 Now John's disciples and those of the Pharisees were fasting; and they came and said to Him, “Why do John's disciples and those of the Pharisees fast, but your disciples do not?”
Almajiran Yahaya da Farisawa suna azumi, sai wadansu mutane suka zo suka ce, “Don me almajiran Yahaya da almajiran Farisawa na azumi amma na ka almajiran ba su yi?”
19 So Jesus said to them: “Can the groomsmen fast while the bridegroom is with them? As long as they have the bridegroom to themselves they cannot fast.
Sai Yesu yace masu, “Abokan ango, za su yi azumi sa'adda ango yake tare da su? muddin suna tare da ango ba za su yi azumi ba.
20 But the time will come when the bridegroom will be taken away from them, and then they will fast, in those days.
Amma kwanaki za su zo da za a dauki angon daga gare su, a wadancan kwanakin ne, za su yi azumi.
21 “Further, no one sews a patch of unshrunk cloth on an old garment, or else the new tears away some of the old, and a worse hole results.
Babu wanda zai dinka sabuwar riga ya hada ta da tsohuwar riga, sai rigar ta yage, kuma ta yi mummunar yagewa.
22 And no one puts new wine into old wineskins, or else the new wine bursts the wineskins, the wine spills out and the skins will be ruined; rather, new wine must be put into new wineskins.”
Babu wanda zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsohuwar salka, ai sai salkar ta fashe kuma ruwan inabin ya zube. duka biyu ruwan inabin da salkar arasa su. A maimakon haka, sai ka sanya sabon ruwan inabi cikin sabuwar salka.”
23 Now it happened, on a Sabbath, that He was passing through some grain fields, and His disciples began to make a path, picking the heads of grain.
A ranar asabar Yesu ya tafi cikin gonakin hatsi, sai almajiransa su ka fara zagar hatsi,
24 So the Pharisees said to Him, “Just look, why are they doing on a Sabbath that which is not permitted?”
Sai Farisawa su ka ce masa, “Duba, don me suke yin abin da bai dace a yi ranar Asabar ba?”
25 And He said to them: “Did you never read what David did when he was in need and hungry, he and those with him?
Yace masu, Ba ku karanta ba abinda Dauda ya yi sa'adda yake jin yunwa, shi da mutanen da ke tare da shi?
26 How he entered the house of God (making Abiathar high priest) and ate the consecrated bread, which only priests are permitted to eat, and shared it with those who were with him?”
Yadda ya shiga gidan Ubangiji, sa'adda Abiyata ya ke babban firist, ya ci gurasa da ke ta firist wadda bai dace wani ya ci ba sai Firistoci. Har kuma ya ba wadanda ke tare da shi.”
27 Then He said to them: “The Sabbath was made for man, not man for the Sabbath.
Yesu yace, “Asabar an yi ta don mutum ne, ba a yi mutum don Asabar ba.
28 Therefore the Son of the Man is Lord even of the Sabbath.”
Saboda haka, Dan Mutum Ubangiji ne, har da na Asabar.”

< Mark 2 >