< Luke 14 >
1 Then it happened, when He entered the house of one of the rulers of the Pharisees to eat bread on the Sabbath, that they were watching Him closely.
Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu.
2 And then, there in front of Him was a man who had dropsy!
Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara.
3 And Jesus reacted by saying to the lawyers and Pharisees, “Is it lawful to heal on the Sabbath?”
Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, “Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?”
4 But they kept silent. So He took hold of him, healed him, and let him go.
Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi.
5 Then He addressed them saying, “Which of you, if a son or an ox falls into a pit, will not immediately pull him out on the Sabbath day?”
Sai yace masu, “Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?”
6 And they could not answer Him regarding these things.
Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
7 Then He told a parable to those who were invited, having observed how they kept trying for the best places, saying to them:
Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu,
8 “Whenever you are invited by someone to a wedding feast, do not recline in the place of honor, in case someone more honorable than you has been invited by him;
“Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja.
9 then he who invited you both will come and say, ‘You, give this man place!’ and then, with shame, you start to take the lowest place.
Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
10 Rather, whenever you are invited, go and recline in the lowest place, so that when your host comes, he may say to you, ‘Friend, move up higher.’ Then you will have honor in the presence of your fellow guests.
Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi.
11 Because everyone who exalts himself will be humbled, and he who humbles himself will be exalted.”
Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi”.
12 Then He said directly to His host: “Whenever you give a dinner or a supper, do not invite your friends, nor your brothers, nor your relatives, nor rich neighbors, lest they also invite you back, and you be repaid.
Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, “Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
13 But whenever you make a banquet, invite the poor, the crippled, the lame, the blind;
Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi,
14 and you will be blessed, because they cannot repay you—you will be repaid at the resurrection of the righteous.”
za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci.”
15 Well when one of the fellow-recliners heard these things, he said to Him, “Blessed is he who will eat dinner in the Kingdom of God!”
Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, “Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!”
16 So He said to him: “A certain man prepared a great banquet and invited many.
Amma Yesu ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.
17 And at meal time he sent his slave to say to those who were invited, ‘Come, because everything is now ready.’
Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, “Ku zo, duk an shirya kome.”
18 But they all alike began to make excuses. The first said to him: ‘I bought a field, and I need to go and see it. I ask you to have me excused.’
Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.'
19 Another said: ‘I bought five yoke of oxen, and I am going to test them. I ask you to have me excused.’
Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.'
20 Yet another said, ‘I have married a wife, and so I cannot come.’
Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
21 So that slave came and reported these things to his master. Then the owner of the house became angry and said to his slave, ‘Go out quickly into the streets and lanes of the city, and bring in here the poor and crippled and blind and lame.’
Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.'
22 And the slave said, ‘Master, what you ordered has been done, and there is still room.’
Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri.”
23 Then the master said to the slave: ‘Go out to the roads and hedges and make people come in, so that my house may be filled.
Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana.
24 For I tell you that none of those men who were invited will get a taste of my banquet!’”
Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina.”
25 Now large crowds were traveling with Him, and turning He said to them:
Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu,
26 “If anyone comes to me and does not hate his father and mother, wife and children, brothers and sisters, yes, and even his own life, he cannot be my disciple.
“Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba.
27 And whoever does not carry his cross, and come after me, cannot be my disciple.
Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 “Further, which of you, intending to build a tower, does not sit down first and calculate the cost, whether he has enough to complete it?
Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin?
29 This so he does not lay a foundation without being able to finish, and all who see it begin to ridicule him,
Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a,
30 saying, ‘This man began to build and was not able to finish!’
su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
31 “Or what king, going to engage another king in battle, does not sit down first and consider whether he is able with ten thousand to meet the one coming against him with twenty thousand?
Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba?
32 And if not, while the other is still far away he sends a delegation and asks for terms for peace.
In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama.
33 “So likewise, any of you who does not renounce all his own possessions cannot be my disciple.
Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina.”
34 Salt is good; but should the salt become insipid, with what can it be seasoned?
“Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi?
35 It is fit for neither soil nor fertilizer; it is thrown out. He who has ears to hear, let him hear!”
Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”