< John 13 >

1 Now before the Feast of the Passover, Jesus, knowing that His hour had come that He should depart from this world to the Father, having loved His own who were in the world He loved them to the end.
Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
2 And after supper (the devil already having put it into the heart of Judas Iscariot, Simon's son, to betray Him),
Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
3 Jesus, knowing that the Father had given everything into His hands, and that He had come from God and was going to God,
Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
4 He gets up from the meal and lays aside His garments, and taking a towel He tied it around Himself.
saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
5 Then He poured water into the basin and began to wash the disciples' feet and to dry them with the towel with which He was wrapped.
Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
6 So He comes to Simon Peter, and he says to Him, “Lord, you wash my feet?!”
Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
7 Jesus answered and said to him, “What I am doing you do not understand now, but you will know [by experience] after this.”
Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
8 Peter says to Him, “You will never ever wash my feet!” Jesus answered him, “If I do not wash you, you have no part with me.” (aiōn g165)
Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn g165)
9 Simon Peter says to Him, “Lord, not only my feet, but also my hands and my head!”
Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
10 Jesus says to him: “One who is bathed has no need except to wash his feet, but is clean all over. And you (pl) are clean, but not all of you.”
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
11 (He knew who was betraying Him; that is why He said, “Not all of you are clean.”)
Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
12 So when Jesus had washed their feet and put His garments back on, He reclined again and said to them: “Do you know what I have done to you?
Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
13 You address me as ‘Teacher’ and ‘Lord’, and you speak correctly, because I am.
Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
14 So then, if I, Lord and Teacher, washed your feet, you also ought to wash one another's feet.
Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
15 Because I have given you an example, so that you also should do just as I did to you.
Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
16 “Most assuredly I say to you, a slave is not greater than his owner, neither is a messenger greater than the one who sent him.
Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
17 If you understand these things, you are blessed if you do them.
Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
18 “I do not speak concerning all of you—I know whom I chose. But let the Scripture be fulfilled: ‘The one eating bread with me lifted up his heel against me.’
“Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
19 I am telling you now before it happens, so that when it does happen you will believe that I am.
“Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
20 Most assuredly I say to you, he who receives whomever I send receives me, and he who receives me receives Him who sent me.”
Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
21 Having said these things, Jesus was distressed in His spirit and testified saying, “Most assuredly I say to you, one of you will betray me!”
Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 So the disciples started looking at each other, at a loss as to whom He meant.
Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
23 Now one of His disciples, whom Jesus loved, was reclining beside Jesus' bosom.
Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
24 So Simon Peter motions to him to inquire whom it might be that He was referring to.
Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
25 And leaning back against Jesus' breast he says to Him, “Lord, who is it?”
Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
26 Jesus answers, “It is the one to whom I will give the piece of dunked bread.” And dunking the bread He gives it to Judas Iscariot, Simon's son.
Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
27 And after the sop, then Satan entered into him. Whereupon Jesus says to him, “What you are doing, do quickly!”
Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
28 (Now none of those reclining at the table knew why He said this to him.
Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
29 Since Judas had the money box, some supposed that Jesus was telling him to buy what they needed for the feast, or to give something to the poor.)
Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
30 So having received the sop, immediately he went out. And it was night.
Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
31 When he had gone out Jesus says: “Now the Son of the Man has been glorified, and God has been glorified in Him.
Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
32 Since God has been glorified in Him, God will also glorify Him with Himself, and He will do so presently.
In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
33 “Little children, I am with you just a little longer. You will look for me, and as I said to the Jews, ‘Where I am going you cannot come,’ so now I say to you.
“’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
34 “I give you a new commandment, that you love one another just as I have loved you—that you also love one another.
“Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
35 By this all will know that you are my disciples, if you have love for one another.”
Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
36 Simon Peter says to Him, “Lord, where are you going?” Jesus answered him, “Where I am going you cannot follow me now, but later you will follow me.”
Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
37 Peter says to Him: “Lord, why can't I follow you now? I will lay down my life for your sake!”
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
38 Jesus answered him: “You will lay down your life for my sake? Most assuredly I say to you, no rooster can crow until you have denied me three times!
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!

< John 13 >