< Galatians 2 >

1 Fourteen years later I went up to Jerusalem again, with Barnabas, taking Titus along as well.
Daga nan, bayan shekara goma sha hudu na koma Urushalima tare da Barnaba. Na kuma dauki Titus tare da ni.
2 I went on the basis of a revelation and set before them [the main apostles] the Gospel that I proclaim among the nations/Gentiles.—Now I did this privately to those with influence, lest somehow I might run, or had run, in vain.
Na koma ne domin Allah ya nuna mani in koma. Sai na gabatar masu shelar bisharan da nake yi a cikin al'ummai. (Amma a kebe na yi magana da wadanda aka dauka muhimman shugabanni). Na yi haka ne domin in tabbatar da cewa ba gudun banza nake yi ba, ko kuma na yi gudun banza.
3 However, not even Titus, who was with me, was compelled to be circumcised, for being a Greek.
Amma ko Titus wanda yake tare da ni, Baheline, ba wanda ya tilasta masa ya yi kaciya.
4 This came up because of the false brothers who were smuggled in (who stole in to spy out our freedom, that we have in Christ Jesus, so as to reduce us to slavery),
Wannan maganar ta taso ne daga 'yan'uwan karya da suka zo cikinmu a boye su ga 'yancin mu a cikin Yesu Almsihu. Sun yi marmarin su maishe mu bayi ga doka.
5 to whom we did not yield, even for a moment, so that the truth of the Gospel might continue with you.—
Ba mu mika kanmu biyayya gare su ba ko da na sa'a daya, domin gaskiyar bishara ta kasance babu canzawa domin ku.
6 Now from those who seemed to be important (whatever they were makes no difference to me; God shows favoritism to no man)—those with influence contributed nothing to me,
Amma su wadanda a ke ganin su da muhimmanci ba su taimaka mani da komai ba. Ko su wanene su bai dame ni ba. Allah ba ya karbar wanda mutane suka fi so.
7 but on the contrary, upon seeing that I had been entrusted with the Gospel for the uncircumcised, just as was Peter for the circumcised
Maimakon haka, suka ga an danka mani shelar bishara ga wadanda ba su da kaciya. Kamar yadda aka ba Bitrus shelar bishara ga masu kaciya.
8 (for He who was at work with Peter for the apostleship to the circumcised was also at work with me for that to the uncircumcised),
Gama Allah wanda yake yin aiki a cikin Bitrus domin manzanci zuwa ga masu kaciya, haka kuma yake aiki ciki na zuwa ga al'ummai.
9 and upon perceiving the grace that had been given to me, James and Cephas and John, those reputed to be pillars, gave me and Barnabas the right hand of fellowship, that we should go to the Gentiles, while they to the Jews.
Da Yakubu, Kefas, da Yahaya, wadanda a ke gani masu gina ikilisiya, suka fahimci alherin da aka ba ni, suka bamu hannun dama na zumunci ni da Barnaba, Sun yi haka ne kawai domin mu mu tafi zuwa wurin al'ummai, su kuma su je wurin masu kaciya.
10 They did ask us to keep remembering the poor, the very thing I also was eager to do.
Suna kuma so mu tuna da matalauta. Ni ma ina da aniyar yin haka.
11 But, when Peter came to Antioch, I opposed him to his face, because he was blameworthy.
Da Kefas ya kai Antakiya, na yi tsayayya da shi a gabansa domin shine ke da kuskure.
12 Before certain men came from James, he used to eat with the Gentiles; but when they came he began to draw back and separate himself, fearing those of the circumcision party.
Da ma Kefas yana cin abinci tare da al'ummai kafin zuwan wasu mutane daga wurin Yakubu. Amma da wadannan mutane suka iso, sai ya dena kuma ya ware kansa daga al'umman. Yana jin tsoron wadannan mutanen da ke bukatar kaciya.
13 And the rest of the Jews played the hypocrite with him as well, so that even Barnabas was carried away with their hypocrisy.
Hakannan ma sauran Yahudawa da suke tare da shi sun bi munafurcin sa. A sakamakon haka Barnaba ma ya bi munafurcin su.
14 So when I saw that they were not walking straight according to the truth of the Gospel, I said to Peter in front of them all: “If you, being a Jew, live like a Gentile and not like a Jew, why do you compel the Gentiles to live like Jews?
Da na ga basu bin gaskiyar da take cikin bisharar, na gaya wa Kefas a gaban su duka, “Idan kai Bayahude ne kana rayuwar ka ta al'ummai a maimakon rayuwar Yahudawa, to ta yaya za ka tilasta wa al'ummai su yi zaman Yahudawa? “
15 We natural Jews (and not ‘Gentile sinners’),
Mu da muke Yahudawa daga haihuwa, ba ''Al'ummai masu zunubi ba.''
16 knowing that a man is not justified by the works of the law but by faith in Jesus Christ, we ourselves have believed into Christ Jesus, so as to be justified by faith in Christ and not by works of the law; because no one will be justified by works of law.
Ku sani fa, babu wanda za a baratar ta ayyukan shari'a. A maimakon haka an baratar da su ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu. Mun zo ga cikin Almasihu Yesu domin mu samu baratarwa ta bangaskiya cikin Almasihu, kuma ba ta ayyukan shari'a ba. Domin ta ayyukan shari'a babu wanda zai samu baratarwa.
17 But if while seeking to be justified in Christ we ourselves were discovered to be sinners, then is Christ a minister of sin? Of course not!
Amma idan mun nemi Allah ya baratar da mu cikin Almasihu, mun samu kanmu masu zunubi kenan, Almasihu ya zama bawan zunubi ne? Ko kadan!
18 “Now if I rebuild the things that I destroyed, I acknowledge that I am a transgressor.
Idan na sake gina dogara ta a kan shari'a, dogarar da na juya wa baya, na nuna kai na mai karya shari'a kenan.
19 For through the law I died to the law in order to live to God.
Ta wurin shari'a na mutu ga shari'a, domin in yi rayuwa irin ta Allah.
20 I have been crucified with Christ, so it is no longer I who live but Christ lives in me; what I now live in this body I live by faith in the Son of God, who loved me and gave Himself in my place.
An giciye ni tare da Almasihu, ba nine ke rayuwa ba kuma, amma Almasihu ke rayuwa a cikina. Rayuwar da nake yi a yanzu a cikin jiki, ina yin ta ne, ta wurin bangaskiya ga dan Allah, wanda ya kaunace ni ya ba da kansa domina.
21 I do not nullify the grace of God; for if righteousness is through the law, then Christ died for nothing!”
Ban yi watsi da alherin Allah ba, domin idan adalci ya wanzu ta wurin shari'a, ashe Almasihu ya mutu a banza kenan.

< Galatians 2 >