< Acts 26 >

1 Then Agrippa said to Paul, “You have permission to speak for yourself.” So Paul stretched out his hand and began his defense:
Sai Agaribas ya ce wa Bulus, “Za ka iya kare kan ka.” Sai Bulus ya daga hannunsa ya fara kare kansa.
2 “I consider myself fortunate, King Agrippa, in that I am to make my defense before you this day concerning the things of which I am accused by the Jews,
“Ina farinciki, ya sarki Agaribas, game da saran da Yahudawa ke kawowa a kaina yau;
3 especially because you are expert in all the Jewish customs and issues; therefore I beg you to hear me patiently.
musamman ma don kai masani ne game da al'adun Yahudawa da al'amuransu. Don haka, ina rokanka ka yi hakuri ka saurare ni.
4 Really, the Jews all know my way of life from my youth, which was spent from the beginning among my own nation in Jerusalem,
Hakika, dukan Yahudawa sun san yadda na yi rayuwa ta daga kurciyata a kasa ta, da kuma Urushalima.
5 since they have known me for a long time, if they were willing to testify, that according to the strictest sect of our religion I lived as a Pharisee.
Sun san ni tun farko, kuma yakamata su yarda cewa na yi rayuwa kamar Bafarase, darikan nan mai tsatsauran ra'ayi ta addininmu.
6 And now I stand here being judged for the hope of the promise made by God to our fathers,
Yanzu ina tsaye a nan dominn a shari'anta ni, saboda alkawalin da Allah ya yi wa ubanninmu.
7 to which our twelve tribes, earnestly serving God night and day, hope to attain. It is because of this hope that I am accused by the Jews, King Agrippa.
Domin wannan shine alkawalin da kabilunmu goma sha biyu suka sa zuciya su karba, yayin da suke yin sujada da himma ga Allah dare da rana. Saboda wanan bege, Sarki Agaribas, Yahudawa ke tuhuma ta.
8 Why should any of you consider it incredible that God raises the dead?
Me ya sa wani zai yi tunani cewa abin mamaki ne Allah ya ta da mattatu?
9 “However, I myself thought that I had to perpetrate many things in opposition to the name of Jesus the Natsorean;
Da, na yi tunanin yin abubuwa gaba da sunan Yesu Banazarat.
10 I actually did this in Jerusalem, and many of the saints I shut up in prison, having received authority from the chief priests; and when they were put to death I cast my vote against them.
Na yi wadanan a Urshalima. Na kulle masu bi da yawa a kurkuku, sanadiyar iko da na samu daga wurin manyan firistoci, kuma da ake kashe su ma, ina ba da goyon baya.
11 Yes, I punished them often in every synagogue, trying to force them to blaspheme; I was so excessively enraged against them that I persecuted them even to foreign cities.
Na wahalshe su sau dayawa a cikin dukan majamiu ina kuma yin kokari in tilasta masu su yi sabo. Na yi gaba mai zafi da su kuma na tsananta masu har zuwa birane na wadansu kasashe.
12 “It was on one of those journeys, as I was going to Damascus with authority and a commission from the chief priests,
A sa'anda nake yin wannan, na tafi Dimashku da izinin manyan firistoci;
13 at midday, O king, as I was on the road, I saw a light from heaven brighter than the sun, blazing around me and those traveling with me.
a cikin tafiyata kuma, da tsakar rana, ya sarki, na ga haske daga sama da ya fi rana sheki, ya haskaka kewaye da ni da kuma wadanda ke tafiya tare da ni.
14 Well we all fell to the ground and I heard a voice speaking to me and saying in the Hebrew language: ‘Saul, Saul, why are you persecuting me? It is hard for you to kick against the goads.’
Da dukanmu muka fadi kasa, na ji wata murya na magana da ni a harshen Ibraniyawa tana cewa, 'Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani? Yana da wuya ka hauri abin da ke mai tsini.'
15 So I said, ‘Who are you, Lord?’ And He said: ‘I am Jesus, whom you are persecuting.
Sai na ce, 'Wanene kai ya Ubangiji?' Ubangiji ya amsa, 'Ni ne Yesu wanda kake tsanantawa.
16 Now get up and stand on your feet; because I have appeared to you for this purpose, to appoint you as a servant and a witness both of the things you have seen and of the things I will reveal to you,
Yanzu ka tashi tsaye domin saboda wannan dalili ne na bayyana gare ka in sanya ka, ka zama bawa da mashaidi na game da abubuwan da ka sani a kaina yanzu da wadanda zan bayyana maka daga bisani;
17 delivering you from ‘the people’ and the ethnic nations, to which I am sending you:
Zan kubutar da kai daga wurin mutane da kuma al'ummai da zan aike ka wurinsu,
18 to open their eyes, so as to bring them back from darkness into light and from the authority of Satan to God, that they may receive forgiveness of sins and an inheritance among those who are sanctified, by faith into me.’
domin ka bude idanunsu ka juyo su daga duhu zuwa haske da daga ikon Shaidan zuwa ga Allah, domin su karbi gafarar zunubai da gado da zan ba wadanda na kebe wa kaina ta wurin bangaskiya gare ni.'
19 Therefore, King Agrippa, I was not disobedient to the heavenly vision
Saboda haka, sarki Agaribas, ban yi rashin biyayya da wahayin da na gani daga sama ba;
20 —first to those in Damascus and Jerusalem, then to all the region of Judea and to the ethnic nations, I still preach: ‘repent and turn back to God, doing works worthy of repentance.’
amma, da farko ga wadanda ke a Dimashku, sa'annan a Urushalima da kasar Yahudiya gaba daya, da dukan Al'ummai, na yi wa'azi domin su tuba su kuma juyo ga Allah, su yi ayyukan da suka chanchanci tuba.
21 That is why the Jews seized me in the temple and tried to kill me.
Domin wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a cikin haikali kuma suke kokari su kashe ni.
22 So then, having experienced the help that is from God, I stand to this day testifying to both small and great, saying nothing beyond what both the prophets and Moses said would happen
Allah ya taimake ni har wa yau, domin in iya tsayawa gaban mutane kanana da manya, in bada shaida game da iyakar abin da annabawa da Musa suka fada zai faru;
23 —that the Messiah would suffer; that as the first to rise from the dead He would proclaim light to both ‘the people’ and the ethnic nations.”
wato lallai Almasihu zai sha wahala, ya kuma zama na farko da za'a rayar daga matattu ya kuma yi shelar haske zuwa ga mutanen Yahudawa da Al'ummai.”
24 Well as he thus made his defense, Festus said with a loud voice: “Paul, you are crazy! Your great learning is driving you insane!”
Da Bulus ya gama kare kansa, Festas ya yi magana da babban murya, “Bulus, kana hauka; yawan iliminka yasa ka hauka.”
25 So he said: “I am not crazy, most excellent Festus; rather I pronounce words of truth and reasonableness.
Amma Bulus ya ce, “Ba na hauka, ya mai girma Festas; amma da karfin zuciya nake fadi kalmomin gaskiya da na natsuwa.
26 For the king knows about these things, before whom I speak freely; for I am convinced that none of this has escaped his notice, since it was not done in a corner.
Saboda sarkin ya san wadannan abubuwa duka; shi ya sa nake magana gabagadi, don na hakikance cewa, ba abin da ke a boye gare shi; gama ba a yi wadannan abubuwa a boye ba.
27 King Agrippa, do you believe the prophets? I know that you believe.”
Ko ka gaskanta da annabawa, Sarki Agaribas? Na sani ka gaskanta.”
28 So Agrippa said to Paul, “You will soon persuade me to become a Christian!”
Agaribas ya ce wa Bulus, “A cikin karamin lokaci kana so ka rinjaye ni ka mai da ni Krista?”
29 So Paul said, “Whether sooner or later, I would to God that not only you but also all who are hearing me this day may become such as I am, except for these chains.”
Bulus ya ce, “Ina roko ga Allah, domin ko a karamin lokaci ko a dogon lokaci, ba kai kadai ba, amma har da wadanda ke sauraro na yau su zama kamar ni, amma ban da wadannan sarkokin.”
30 Upon his saying this, the king stood up, along with the governor and Bernice and those sitting with them;
Sai sarki ya tashi tsaye tare da gwamna da Barniki da dukan wadanda ke zaune tare da su;
31 and when they had withdrawn they started talking among themselves, saying, “This man is doing nothing deserving of death or chains.”
da suka bar dakin taron, suka ci gaba da magana da juna suna cewa, “Wannan mutum bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ko kuma dauri ba.”
32 And Agrippa said to Festus, “This man could have been set free, if he had not appealed to Caesar.”
Agaribas ya ce wa Fastos, “Da mutumin nan bai daukaka kara zuwa ga Kaisar ba da an sake shi.”

< Acts 26 >