< 2 John 1 >

1 The elder, to the elect lady and her children, whom I love in truth—and not I only, but also all who have known the Truth—
Daga dattijon zuwa ga uwar gida zababbiya da yayanta, wadanda nake kauna da gaskiya, ba ni kadai ba, amma da dukan wadanda sun san gaskiya -
2 because of the Truth, who abides in us and will be with us into the age: (aiōn g165)
domin gaskiya da take cikinmu za ta kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn g165)
3 Grace, mercy and peace from God the Father and from the Lord Jesus Christ, the Son of the Father, will be with you in truth and love.
Alheri da jinkai da salama za su kasance tare da mu, daga Allah Uba da kuma daga Yesu Almasihu Dan Uba, a cikin gaskiya da kauna.
4 It has given me great joy to find some of your children walking in truth, just as we received commandment from the Father.
Na yi murna sosai sa'anda na sami wadansu yayanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda muka karbi wannan umarni daga Uba.
5 And now I put a request to you, lady (not as though writing a new commandment to you, but one that we have from the beginning): that we love one another.
Yanzu ina rokon ki, uwar gida, ba kamar ina rubuta maki sabon umarni ba, amma wannan da muka samu tun da can, cewa mu kaunaci junanmu.
6 And this is the love, that we live according to His commandments—this is the commandment, just as you heard from the beginning, that you should live according to it.
Wannan kuma itace kauna, cewa mu yi tafiya bisa ga umarnin sa. Wannan shine umarnin, daidai kamar yadda kuka ji da fari, da cewa ku yi tafiya a cikinsa.
7 Now many deceivers have come into the world, who do not acknowledge Jesus Christ as coming in flesh—this is the deceiver, even the Antichrist!
Gama masu yaudara sun fito a duniya, wadanda ba su yarda cewa Yesu ya zo cikin jiki ba. Wannan ne mayaudari da kuma magabcin Almasihu.
8 Look to yourselves, so that we not lose the things for which we worked but may receive a full reward.
Ku dubi kanku, domin kada ku rasa abubuwan da mu duka muka yi aiki a kansu, amma domin ku karba dukan sakamon ku.
9 Anyone who turns aside and does not continue in the teaching of Christ does not have God; but whoever continues in Christ's teaching does have both the Father and the Son.
Duk wanda ya ci gaba da tafiya ba cikin koyarwa Almasihu ba, ba shi da Allah. Wanda ya zauna cikin koyarwar kwa yana tare da Uban da kuma Dan.
10 If anyone comes to you and does not bring this teaching, do not receive him into your house; do not even tell him, “I wish you well,”
Duk wanda ya zo wurinku, ba tare da wannan koyarwar ba, kar ku karbe shi cikin gidanku, kada ma ku gaishe shi.
11 because whoever tells him, “I wish you well,” participates in his malignant works.
Domin duk wanda ya gaishe shi ya yi tarayya da shi kenan cikin miyagun ayyukan sa.
12 Although I had many things to write to you, I did not wish to do so with paper and ink; instead I hope to come to you and speak face to face, so that our joy may be complete.
Ina da abubuwa dayawa da nake so in rubuta maki amma al'kalami tawada da takarda baza su iya daukar su duka ba. Amma duk da haka ina begen zuwa gare ki domin mu yi magana fuska da fuska, domin farin cikn mu ya zama cikakke.
13 The children of your elect sister greet you. Amen.
Yayan yar'uwarki zababbiya suna gaishe ki.

< 2 John 1 >