< 1 Corinthians 11 >

1 Become my imitators, just as I am Christ's.
Ku yi koyi da ni, kamar yadda nake koyi da Almasihu.
2 Now I praise you, brothers, that you remember me in all things and hold the traditions just as I delivered them to you.
Yanzu ina yaba maku ne, don kuna tunawa da ni cikin abu duka. Ina kuma yaba maku wajen bin al'adun da na ba ku daidai yadda na ba ku.
3 But I want you to know that the head of every man is Christ, while a wife's head is the man and Christ's head is God.
Amma fa ina son ku fahimta da cewa, shugaban kowane mutum Almasihu ne, shugaban kowace mace mutumin ne, shugaban Almasihu Allah ne.
4 Every man who prays or prophesies with his head covered dishonors his head.
Kuma duk mutumin da ya yi addu'a ko annabci kansa a rufe, ya wulakanta shugabansa.
5 But every woman who prays or prophesies with her head uncovered dishonors her own head—it is one and the same as if it had been shaved.
Amma duk macen da ta yi addu'a ko annabci kanta a bude, ta wulakanta shugabanta. Gama yayi dai dai da idan tayi aski.
6 So if a woman does not cover herself, let her also be shorn. But if it is shameful for a woman to be shorn or shaved, let her be covered.
Gama idan mace ba zata rufe kanta ba, to ta yanke gashinta ya zama gajere. Idan abin kunya ne mace ta yanke gashinta ko ta aske kanta, bari ta rufe kanta.
7 Indeed, a man ought not to cover his head, since he is the image and glory of God; but woman is the glory of man.
Bai kamata na miji ya rufe kansa ba, tun da yake shi siffa ne da daukakar Allah. Amma mace daukakar namiji ce.
8 For man did not come from woman, but woman from man;
Don kuwa namiji ba daga jikin mace yake ba. A maimako, matar daga jikin namiji take.
9 and neither was man created for the woman, but woman for the man
Ba a kuma halicci namiji don mace ba. A maimako, an halicci mace don namiji.
10 —for this reason the woman needs to have authority upon her head, because of the angels—
Shi ya sa mace za ta kasance da alamar iko a kanta, saboda mala'iku.
11 nevertheless, in the Lord neither is man independent of woman nor woman independent of man.
Duk da haka, a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, haka kuma namiji ba a rabe yake da mace ba.
12 Because as the woman came from the man, so also the man comes through the woman; but all things are from God.
Kamar yadda mace take daga namiji, haka ma namiji kuma haihuwar mace ne. Amma dukkan abubuwa daga Allah suke.
13 Judge among yourselves: is it proper for a woman to pray to God uncovered?
Ku hukunta da kanku: Daidai ne mace ta yi addu'a ga Allah kanta a bude?
14 Does not nature itself teach you that if a man has long hair, it is a dishonor to him?
Ashe, ko dabi'a bata nuna maku cewa abin kunya ne namiji, ya kasance da dogon gashi ba?
15 But if a woman has long hair, it is a glory to her, because that hair has been given for a covering.
Ba dabi'a ta koya maku cewa idan mace tana da dogon gashi, daukakar ta ne ba? Gama domin rufewa aka yi mata baiwar gashin.
16 But if anyone decides to be contentious, neither we nor the congregations of God have any other practice.
To idan wani yana da niyyaryin gardama game da wannan, mu dai bamu da wata al'adar, ikilisiyoyin Allah kuma haka.
17 Now in giving the following instruction I do not praise you, since you are not coming together for the better but for the worse.
Amma game da umarnin dake biye, ban yaba maku ba, taruwarku ba ta kirki ba ce, ta rashin gaskiya ce.
18 Because, to begin, I hear that when you come together in an assembly there are divisions among you, and I partly believe it.
Farko dai sa'adda kuke, taron ikklisiya, na ji har akwai rarrabuwa tsakaninku, har na fara amincewa da maganar.
19 For there would really need to be factions among you so that the ‘approved’ ones may be recognized among you.
Dole ne a sami tsattsaguwa a tsakaninku, don a iya gane wadanda suke amintattu a cikinku.
20 So when you come together in one place, it is not to eat the Lord's Supper.
Domin, in kun taru a wuri daya, ba jibin Ubangiji kuke ci ba!
21 Because in eating, each one tries to get his meal first, and one goes hungry while another gets drunk!
Ya yin da kuke ci, kowa na cin abincinsa ne kamin sauran Wani yana jin yunwa, wani kuma ya zarin ci, har ya bugu.
22 Now really, do you not have houses to eat and drink in? Or do you despise God's congregation, and humiliate those who have nothing? What shall I say to you? Shall I praise you in this? Indeed not!
Baku da gidajen da zaku ci ku sha, kuna raina ikkilisiyar Allah, kuna kuma wulakanta wa wadanda basu da komai? To, me zan ce maku? Yaba maku zan yi? Ba zan yaba maku ba akan wannan.
23 For I received from the Lord that which I also transmitted to you: The Lord Jesus, during the night in which He was betrayed, took bread;
Amma abin da na karba a gun Ubangiji shi nake baku cewa Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi ya dauki gurasa.
24 and when He had given thanks, He broke it and said: “Take, eat; this is my body that is being broken on your behalf; do this in remembrance of me.”
Bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “wanna shi ne jikina wanda yake saboda ku, ku yi domin tunawa da ni.”
25 In the same way, after they had dined, He took the cup, saying: “This cup is the new covenant in my blood; do this, whenever you drink it, in remembrance of me.”
Ta wannan hanya kuma, sai ya dauki kokon, ya ce, “kokon nan na sabon alkawari ne, da aka tabbatar da shi da cikin jinina. Ku yi haka kuna sha don tunawa da ni.”
26 For whenever you eat this bread and drink this cup, you proclaim the Lord's death, until He comes.
Duk sa'adda kuke cin gurasar nan, kuna kuma sha cikin kokon nan, kuna bayyana mutuwar Ubangiji ke nan, har sai ya dawo.
27 So then whoever eats this bread or drinks the Lord's cup unworthily will be guilty of the body and of the blood of the Lord.
Saboda haka duk wanda ya ci gurasar nan, ko ya sha a cikin kokon nan, na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulakanta jikin Ubangiji da jininsa.
28 But let a man examine himself, and then let him eat of the bread and drink of the cup.
Sai kowa ya fara auna kansa, kafin ya ci gurasar, ya kuma sha a cikin kokon nan.
29 Because he who eats and drinks unworthily eats and drinks judgment to himself, not distinguishing the Lord's body.
In kowa ya ci, ya sha ba tare da rarrabewa da jikin Ubangiji ba, lalle ya jawowa kansa hukunci, ta wurin ci da sha da ya yi.
30 Because of this many among you are weak and sick, and a good many have died.
Shi ya sa da yawa a cikin ku suke raunana, kuma suna fama da rashin lafiya, har ma wasun ku da dama suka yi barci.
31 If we would judge ourselves, we would not be judged.
Amma, in mun auna kanmu, ba a za a hukunta mu ba.
32 But when we are judged, we are disciplined by the Lord, so that we may not be condemned with the world.
In kuwa Ubangiji ne ya ke hukunta mu, To, muna horuwa ke nan, don kada a kayar damu tare da duniya.
33 So then, my brothers, when you come together to eat, wait for one another.
Saboda haka, ya ku 'yan'uwana, idan kuka tattaru don cin abinci, sai ku jira juna.
34 But if anyone is hungry, let him eat at home, lest you come together into judgment. And the rest I will set in order when I come.
Idan kuwa wani yana jin yunwa, ya ci a gida, kada ya zama taronku ya jawo maku hukunci. Batun sauran abubuwan da kuka rubuta kuwa, zan ba da umarni a kai sa'ad da na zo.

< 1 Corinthians 11 >