< Zechariah 6 >

1 And I turned, and lifted up my eyes, and saw: and behold four chariots came out from the midst of two mountains: and the mountains were mountains of brass.
Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
2 In the first chariot were red horses, and in the second chariot black horses.
Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
3 And in the third chariot white horses, and in the fourth chariot grisled horses, and strong ones.
ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
4 And I answered, and said to the angel that spoke in me: What are these, my lord?
Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
5 And the angel answered, and said to me: These are the four winds of the heaven, which go forth to stand before the Lord of all the earth.
Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
6 That in which were the black horses went forth into the land of the north, and the white went forth after them: and the grisled went forth to the land of the south.
Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
7 And they that were most strong, went out, and sought to go, and to run to and fro through all the earth. And he said: Go, walk throughout the earth: and they walked throughout the earth.
Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
8 And he called me, and spoke to me, saying: Behold they that go forth into the land of the north, have quieted my spirit in the land of the north.
Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
9 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
10 Take of them of the captivity, of Holdai, and of Tobias, and of Idaias; thou shalt come in that day, and shalt go into the house of Josias, the son of Sophonias, who came out of Babylon.
“Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
11 And thou shalt take gold and silver: and shalt make crowns, and thou shalt set them on the head of Jesus the son of Josedec, the high priest.
Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
12 And thou shalt speak to him, saying: Thus saith the Lord of hosts, saying: BEHOLD A MAN, THE ORIENT IS HIS NAME: and under him shall he spring up, and shall build a temple to the Lord.
Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
13 Yea, he shall build a temple to the Lord: and he shall bear the glory, and shall sit, and rule upon his throne: and he shall be a priest upon his throne, and the counsel of peace shall be between them both.
Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
14 And the crowns shall be to Helem, and Tobias, and Idaias, and to Hem, the son of Sophonias, a memorial in the temple of the Lord.
Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
15 And they that are far off, shall come and shall build in the temple of the Lord: and you shall know that the Lord of hosts sent me to you. But this shall come to pass, if hearing you will hear the voice of the Lord your God.
Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”

< Zechariah 6 >