< Revelation 11 >
1 And there was given me a reed like unto a rod: and it was said to me: Arise, and measure the temple of God, and the altar and them that adore therein.
Aka ba ni ƙara kamar sandan awo aka kuma ce mini, “Tafi ka auna haikalin Allah da bagaden, ka kuma ƙirga waɗanda suke sujada a can.
2 But the court, which is without the temple, cast out, and measure it not: because it is given unto the Gentiles, and the holy city they shall tread under foot two and forty months:
Sai dai kada ka haɗa da harabar waje; kada ka auna ta, domin an ba da ita ga Al’ummai. Za su tattaka birni mai tsarki har watanni 42.
3 And I will give unto my two witnesses, and they shall prophesy a thousand two hundred sixty days, clothed in sackcloth.
Zan kuma ba wa shaiduna nan biyu iko, za su kuwa yi annabci na kwanaki 1,260, saye da gwadon makoki.”
4 These are the two olive trees, and the two candlesticks, that stand before the Lord of the earth.
Waɗannan su ne itatuwan zaitun biyu da kuma alkukai biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
5 And if any man will hurt them, fire shall come out of their mouths, and shall devour their enemies. And if any man will hurt them, in this manner must he be slain.
Duk wanda ya yi ƙoƙari yin musu lahani, wuta za tă fito daga bakunansu ta cinye abokan gābansu. Haka ne duk mai niyyar yin musu lahani zai mutu.
6 These have power to shut heaven, that it rain not in the days of their prophecy: and they have power over waters to turn them into blood, and to strike the earth with all plagues as often as they will.
Waɗannan mutane suna da iko su kulle sararin sama don kada a yi ruwan sama a lokacin da suke annabci; suna kuma da iko su juye ruwaye su zama jini su kuma bugi duniya da kowace irin annoba a duk lokacin da suke so.
7 And when they shall have finished their testimony, the beast, that ascendeth out of the abyss, shall make war against them, and shall overcome them, and kill them. (Abyssos )
To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos )
8 And their bodies shall lie in the streets of the great city, which is called spiritually, Sodom and Egypt, where their Lord also was crucified.
Gawawwakinsu za su kasance a kwance a titin babban birni, wanda a misalce ake kira Sodom da Masar, inda kuma aka gicciye Ubangijinsu.
9 And they of the tribes, and peoples, and tongues, and nations, shall see their bodies for three days and a half: and they shall not suffer their bodies to be laid in sepulchres.
Kwana uku da rabi mutane daga kowace jama’a, kabila, harshe da kuma al’umma za su yi ta kallon gawawwakinsu su kuma ƙi binne su.
10 And they that dwell upon the earth shall rejoice over them, and make merry: and shall send gifts one to another, because these two prophets tormented them that dwelt upon the earth.
Mazaunan duniya za su ƙyaface su kuma yi biki ta wurin aika kyautai wa juna, domin waɗannan annabawan nan biyu ne suka azabtar da mazaunan duniya.
11 And after three days and a half, the spirit of life from God entered into them. And they stood upon their feet, and great fear fell upon them that saw them.
Amma bayan kwana uku da rabi ɗin numfashin rai daga Allah ya shige su, suka kuwa tashi tsaye, tsoro kuma ya kama waɗanda suka gan su.
12 And they heard a great voice from heaven, saying to them: Come up hither. And they went up to heaven in a cloud: and their enemies saw them.
Sai suka ji wata babbar murya daga sama tana ce musu, “Ku hauro nan.” Suka kuwa haura zuwa sama cikin girgije, yayinda abokan gābansu suna kallo.
13 And at that hour there was made a great earthquake, and the tenth part of the city fell: and there were slain in the earthquake names of men seven thousand: and the rest were cast into a fear, and gave glory to the God of heaven.
A wannan sa’a aka yi wata babbar girgizar ƙasa kashi ɗaya bisa goma kuma na birnin ya rushe. Aka kashe mutane dubu bakwai a girgizar ƙasar, waɗanda suka tsira kuwa suka ji tsoro suka ɗaukaka Allah na sama.
14 The second woe is past: and behold the third woe will come quickly.
Kaito na biyu ya wuce; kaito na uku yana zuwa ba da daɗewa ba.
15 And the seventh angel sounded the trumpet: and there were great voices in heaven, saying: The kingdom of this world is become our Lord’s and his Christ’s, and he shall reign for ever and ever. Amen. (aiōn )
Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn )
16 And the four and twenty ancients, who sit on their seats in the sight of God, fell on their faces and adored God, saying:
Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa suka kuma yi wa Allah sujada,
17 We give thee thanks, O Lord God Almighty, who art, and who wast, and who art to come: because thou hast taken to thee thy great power, and thou hast reigned.
suna cewa, “Muna maka godiya ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, domin ka karɓi ikonka mai girma ka kuma fara mulki.
18 And the nations were angry, and thy wrath is come, and the time of the dead, that they should be judged, and that thou shouldest render reward to thy servants the prophets and the saints, and to them that fear thy name, little and great, and shouldest destroy them who have corrupted the earth.
Al’ummai suka yi fushi; fushinka kuwa ya zo. Lokaci ya yi don a shari’anta matattu, da kuma don sākawa wa bayinka annabawa da tsarkakanka da kuma su waɗanda suke girmama sunanka, ƙarami da babba, don kuma hallakar da waɗanda suka hallaka duniya.”
19 And the temple of God was opened in heaven: and the ark of his testament was seen in his temple, and there were lightnings, and voices, and an earthquake, and great hail.
Sa’an nan aka buɗe haikalin Allah da yake a sama, kuma a cikin haikalinsa aka ga akwatin alkawarinsa. Sai kuwa ga walƙiya, ƙararraki, tsawa, girgizar ƙasa, da kuma ƙanƙara masu girma.