< Revelation 10 >
1 And I saw another mighty angel come down from heaven, clothed with a cloud, and a rainbow was on his head, and his face was as the sun, and his feet as pillars of fire.
Sa'anan na ga wani babban mala'ika yana zuwa daga sama. Yana lullube cikin girgije, a bisa kansa akwai bakangizo. Fuskarsa kamar rana, kafafunsa kamar ginshikan wuta.
2 And he had in his hand a little book open: and he set his right foot upon the sea, and his left foot upon the earth.
Yana rike da karamin littafi a hannunsa, da aka bude, sai ya sa kafarsa ta dama a bisa teku, kafarsa ta hagu kuma a kan kasa.
3 And he cried with a loud voice as when a lion roareth. And when he had cried, seven thunders uttered their voices.
Sai yayi ihu da babbar murya kamar zaki mai ruri. Lokacin da ya yi ihu, tsawan nan bakwai suka yi magana da karar su.
4 And when the seven thunders had uttered their voices, I was about to write: and I heard a voice from heaven saying to me: Seal up the things which the seven thunders have spoken; and write them not.
Da tsawan nan bakwai suka yi magana, ina dab da rubutu, amma na ji wata murya daga sama cewa, “Ka rike asirin abin da tsawan nan bakwai suka fada. Kada ka rubuta shi.”
5 And the angel, whom I saw standing upon the sea and upon the earth, lifted up his hand to heaven,
Sai mala'ikan da na gani tsaye bisa teku da kasa, ya daga hannun damarsa sama.
6 And he swore by him that liveth for ever and ever, who created heaven, and the things which are therein; and the earth, and the things which are in it; and the sea, and the things which are therein: That time shall be no longer. (aiōn )
Sai ya rantse da wannan da ke raye har abada abadin - wanda ya halicci sama da duk abinda ke cikinsa, da duniya da duk abin da ke a kanta, da teku da dukan abin da ke cikinsa, sai mala'ikan ya ce, “Babu sauran jinkiri. (aiōn )
7 But in the days of the voice of the seventh angel, when he shall begin to sound the trumpet, the mystery of God shall be finished, as he hath declared by his servants the prophets.
Amma a ranar da mala'ika na bakwai yana dab da busa kahonsa, a lokacin ne asirin Allah zai cika, daidai da yadda ya sanar wa bayinsa annabawa.”
8 And I heard a voice from heaven again speaking to me, and saying: Go, and take the book that is open, from the hand of the angel who standeth upon the sea, and upon the earth.
Muryar da na ji daga sama ta sake magana da ni: “Tafi, ka dauki budadden littafin da ke hannun mala'ikan da ke tsaye bisa teku da kan kasa.”
9 And I went to the angel, saying unto him, that he should give me the book. And he said to me: Take the book, and eat it up: and it shall make thy belly bitter, but in thy mouth it shall be sweet as honey.
Sai na tafi wurin mala'ikan na ce da shi ka bani karamin littafin. Yace dani, “Dauki littafin ka ci. Zai sa cikinka ya yi daci, amma a bakinka zai yi zaki kamar zuma.”
10 And I took the book from the hand of the angel, and ate it up: and it was in my mouth, sweet as honey: and when I had eaten it, my belly was bitter.
Na dauki karamin littafin daga hannun mala'ikan na ci. Ya yi zaki sosai a bakina kamar zuma, amma da na ci, sai cikina ya zama da daci.
11 And he said to me: Thou must prophesy again to many nations, and peoples, and tongues, and kings.
Wani yace mani, “Dole ka sake yin annabci kuma game da mutane masu yawa, da al'ummai, da harsuna da sarakuna.”