< Psalms 92 >

1 A psalm of a canticle on the sabbath day. It is good to give praise to the Lord: and to sing to thy name, O most High.
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 To shew forth thy mercy in the morning, and thy truth in the night:
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 Upon an instrument of ten strings, upon the psaltery: with a canticle upon the harp.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 For thou hast given me, O Lord, a delight in thy doings: and in the works of thy hands I shall rejoice.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 O Lord, how great are thy works! thy thoughts are exceeding deep.
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 The senseless man shall not know: nor will the fool understand these things.
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 When the wicked shall spring up as grass: and all the workers of iniquity shall appear: That they may perish for ever and ever:
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 But thou, O Lord, art most high for evermore.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 For behold thy enemies, O Lord, for behold thy enemies shall perish: and all the workers of iniquity shall be scattered.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 But my horn shall be exalted like that of the unicorn: and my old age in plentiful mercy.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 My eye also hath looked down upon my enemies: and my ear shall hear of the downfall of the malignant that rise up against me.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 The just shall flourish like the palm tree: he shall grow up like the cedar of Libanus.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 They that are planted in the house of the Lord shall flourish in the courts of the house of our God.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 They shall still increase in a fruitful old age: and shall be well treated,
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 That they may shew, That the Lord our God is righteous, and there is no iniquity in him.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Psalms 92 >