< Psalms 9 >

1 Unto the end, for the hidden things of the Son. A psalm for David. I will give praise to thee, O Lord, with my whole heart: I will relate all thy wonders.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
2 I will be glad and rejoice in thee: I will sing to thy name, O thou most high.
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
3 When my enemy shall be turned back: they shall be weakened and perish before thy face.
Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
4 For thou hast maintained my judgment and my cause: thou hast sat on the throne, who judgest justice.
Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
5 Thou hast rebuked the Gentiles, and the wicked one hath perished: thou hast blotted out their name for ever and ever.
Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
6 The swords of the enemy have failed unto the end: and their cities thou hast destroyed. Their memory hath perished with a noise.
Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
7 But the Lord remaineth for ever. He hath prepared his throne in judgment:
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8 And he shall judge the world in equity, he shall judge the people in justice.
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9 And the Lord is become a refuge for the poor: a helper in due time in tribulation.
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10 And let them trust in thee who know thy name: for thou hast not forsaken them that seek thee, O Lord.
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
11 Sing ye to the Lord, who dwelleth in Sion: declare his ways among the Gentiles:
Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
12 For requiring their blood he hath remembered the: he hath not forgotten the cry of the poor.
Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
13 Have mercy on me, O Lord: see my humiliation which I suffer from my enemies.
Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
14 Thou that liftest me up from the gates of death, that I may declare all thy praises in the gates of the daughter of Sion.
don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
15 I will rejoice in thy salvation: the Gentiles have stuck fast in the destruction which they have prepared. Their foot hath been taken in the very snare which they hid.
Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
16 The Lord shall be known when he executeth judgments: the sinner hath been caught in the works of his own hands.
An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
17 The wicked shall be turned into hell, all the nations that forget God. (Sheol h7585)
Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
18 For the poor man shall not be forgotten to the end: the patience of the poor shall not perish for ever.
Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
19 Arise, O Lord, let not man be strengthened: let the Gentiles be judged in thy sight.
Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
20 Appoint, O Lord, a lawgiver over them: that the Gentiles may know themselves to be but men.
Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)

< Psalms 9 >