< Psalms 86 >
1 A prayer for David himself. Incline thy ear, O Lord, and hear me: for I am needy and poor.
Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
2 Preserve my soul, for I am holy: save thy servant, O my God, that trusteth in thee.
Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
3 Have mercy on me, O Lord, for I have cried to thee all the day.
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
4 Give joy to the soul of thy servant, for to thee, O Lord, I have lifted up my soul.
Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
5 For thou, O Lord, art sweet and mild: and plenteous in mercy to all that call upon thee.
Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
6 Give ear, O Lord, to my prayer: and attend to the voice of my petition.
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
7 I have called upon thee in the day of my trouble: because thou hast heard me.
A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
8 There is none among the gods like unto thee, O Lord: and there is none according to thy works.
A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
9 All the nations thou hast made shall come and adore before thee, O Lord: and they shall glorify thy name.
Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
10 For thou art great and dost wonderful things: thou art God alone.
Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
11 Conduct me, O Lord, in thy way, and I will walk in thy truth: let my heart rejoice that it may fear thy name.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
12 I will praise thee, O Lord my God: with my whole heart, and I will glorify thy name for ever:
Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
13 For thy mercy is great towards me: and thou hast delivered my soul out of the lower hell. (Sheol )
Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol )
14 O God, the wicked are risen up against me, and the assembly of the mighty have sought my soul: and they have not set thee before their eyes.
Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
15 And thou, O Lord, art a God of compassion, and merciful, patient, and of much mercy, and true.
Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
16 O look upon me, and have mercy on me: give thy command to thy servant, and save the son of thy handmaid.
Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
17 Shew me a token for good: that they who hate me may see, and be confounded, because thou, O Lord, hast helped me and hast comforted me.
Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.