< Psalms 84 >

1 Unto the end, for the winepresses, a psalm for the sons of Core. How lovely are thy tabernacles, O Lord of host!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
2 My soul longeth and fainteth for the courts of the Lord. My heart and my flesh have rejoiced in the living God.
Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
3 For the sparrow hath found herself a house, and the turtle a nest for herself where she may lay her young ones: Thy altars, O Lord of hosts, my king and my God.
Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
4 Blessed are they that dwell in thy house, O Lord: they shall praise thee for ever and ever.
Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
5 Blessed is the man whose help is from thee: in his heart he hath disposed to ascend by steps,
Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
6 In the vale of tears, in the place which be hath set.
Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
7 For the lawgiver shall give a blessing, they shall go from virtue to virtue: the God of gods shall be seen in Sion.
Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
8 O Lord God of hosts, hear my prayer: give ear, O God of Jacob.
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
9 Behold, O God our protector: and look on the face of thy Christ.
Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
10 For better is one day in thy courts above thousands. I have chosen to be an abject in the house of my God, rather than to dwell in the tabernacles of sinners.
Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
11 For God loveth mercy and truth: the Lord will give grace and glory.
Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
12 He will not deprive of good things them that walk in innocence: O Lord of hosts, blessed is the man that trusteth in thee.
Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.

< Psalms 84 >