< Psalms 83 >
1 A canticle of a psalm for Asaph. O God, who shall be like to thee? hold not thy peace, neither be thou still, O God.
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 For lo, thy enemies have made a noise: and they that hate thee have lifted up the head.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 They have taken a malicious counsel against thy people, and have consulted against thy saints.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 They have said: Come and let us destroy them, so that they be not a nation: and let the name of Israel be remembered no more.
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 For they have contrived with one consent: they have made a covenant together against thee,
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 The tabernacles of the Edomites, and the Ismahelites: Moab, and the Agarens,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal, and Ammon and Amalec: the Philistines, with the inhabitants of Tyre.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Yea, and the Assyrian also is joined with them: they are come to the aid of the sons of Lot.
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Do to them as thou didst to Madian and to Sisara: as to Jabin at the brook of Cisson.
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Who perished at Endor: and became as dung for the earth.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Make their princes like Oreb, and Zeb, and Zebee, and Salmana. All their princes,
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 Who have said: Let us possess the sanctuary of God for an inheritance.
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 O my God, make them like a wheel; and as stubble before the wind.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 As fire which burneth the wood: and as a flame burning mountains:
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 So shalt thou pursue them with thy tempest: and shalt trouble them in thy wrath.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Fill their faces with shame; and they shall seek thy name, O Lord.
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Let them be ashamed and troubled for ever and ever: and let them be confounded and perish.
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 And let them know that the Lord is thy name: thou alone art the most High over all the earth.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.