< Psalms 81 >
1 Unto the end, for the winepresses, a psalm for Asaph himself. Rejoice to God our helper: sing aloud to the God of Jacob.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Take a psalm, and bring hither the timbrel: the pleasant psaltery with the harp.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Blow up the trumpet on the new moon, on the noted day of your solemnity.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 For it is a commandment in Israel, and a judgment to the God of Jacob.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 He ordained it for a testimony in Joseph, when he came out of the land of Egypt: he heard a tongue which he knew not.
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 He removed his back from the burdens: his hands had served in baskets.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 Thou calledst upon me in affliction, and I delivered thee: I heard thee in the secret place of tempest: I proved thee at the waters of contradiction.
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Hear, O my people, and I will testify to thee: O Israel, if thou wilt hearken to me,
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 There shall be no new god in thee: neither shalt thou adore a strange god.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 For I am the Lord thy God, who brought thee out of the land of Egypt: open thy mouth wide, and I will fill it.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 But my people heard not my voice: and Israel hearkened not to me.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 So I let them go according to the desires of their heart: they shall walk in their own inventions.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 If my people had heard me: if Israel had walked in my ways:
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 I should soon have humbled their enemies, and laid my hand on them that troubled them.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 The enemies of the Lord have lied to him: and their time shall be for ever.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 And he fed them with the fat of wheat, and filled them with honey out of the rock.
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”