< Psalms 73 >

1 A psalm for Asaph. How good is God to Israel, to them that are of a right heart!
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 But my feet were almost moved; my steps had well nigh slipped.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 Because I had a zeal on occasion of the wicked, seeing the prosperity of sinners.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 For there is no regard to their death, nor is there strength in their stripes.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 They are not in the labour of men: neither shall they be scourged like other men.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Therefore pride hath held them fast: they are covered with their iniquity and their wickedness.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Their iniquity hath come forth, as it were from fatness: they have passed into the affection of the heart.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 They have thought and spoken wickedness: they have spoken iniquity on high.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 They have set their mouth against heaven: and their tongue hath passed through the earth.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Therefore will my people return here and full days shall be found in them.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 And they said: How doth God know? and is there knowledge in the most High?
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Behold these are sinners; and yet abounding in the world they have obtained riches.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 And I said: Then have I in vain justified my heart, and washed my hands among the innocent.
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 And I have been scourged all the day; and my chastisement hath been in the mornings.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 If I said: I will speak thus; behold I should condemn the generation of thy children.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 I studied that I might know this thing, it is a labour in my sight:
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 Until I go into the sanctuary of God, and understand concerning their last ends.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 But indeed for deceits thou hast put it to them: when they were lifted up thou hast cast them down.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 How are they brought to desolation? they have suddenly ceased to be: they have perished by reason of their iniquity.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 As the dream of them that awake, O Lord; so in thy city thou shalt bring their image to nothing.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 For my heart hath been inflamed, and my reins have been changed:
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 And I am brought to nothing, and I knew not.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 I am become as a beast before thee: and I am always with thee.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 Thou hast held me by my right hand; and by thy will thou hast conducted me, and with thy glory thou hast received me.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 For what have I in heaven? and besides thee what do I desire upon earth?
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 For thee my flesh and my heart hath fainted away: thou art the God of my heart, and the God that is my portion for ever.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 For behold they that go far from thee shall perish: thou hast destroyed all them that are disloyal to thee.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 But it is good for me to adhere to my God, to put my hope in the Lord God: That I may declare all thy praises, in the gates of the daughter of Sion.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< Psalms 73 >