< Psalms 70 >
1 Unto the end, a psalm for David, to bring to remembrance that the Lord saved him. O God, come to my assistance; O Lord, make haste to help me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
2 Let them be confounded and ashamed that seek my soul:
Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
3 Let them be turned backward, and blush for shame that desire evils to me: Let them be presently turned away blushing for shame that say to me: Tis well, tis well.
Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
4 Let all that seek thee rejoice and be glad in thee; and let such as love thy salvation say always: The Lord be magnified.
Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
5 But I am needy and poor; O God, help me. Thou art my helper and my deliverer: O Lord, make no delay.
Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.