< Psalms 69 >

1 Unto the end, for them that shall be changed; for David. SAVE me, O God: for the waters are come in even unto my soul.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 I stick fast in the mire of the deep: and there is no sure standing. I am come into the depth of the sea: and a tempest hath overwhelmed me.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 I have laboured with crying; my jaws are become hoarse: my eyes have failed, whilst I hope in my God.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 They are multiplied above the hairs of my head, who hate me without cause. My enemies are grown strong who have wrongfully persecuted me: then did I pay that which I took not away.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 O God, thou knowest my foolishness; and my offences are not hidden from thee:
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 Let not them be ashamed for me, who look for thee, O Lord, the Lord of hosts. Let them not be confounded on my account, who seek thee, O God of Israel.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 Because for thy sake I have borne reproach; shame hath covered my face.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 I am become a stranger to my brethren, and an alien to the sons of my mother.
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 For the zeal of thy house hath eaten me up: and the reproaches of them that reproached thee are fallen upon me.
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 And I covered my soul in fasting: and it was made a reproach to me.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 And I made haircloth my garment: and I became a byword to them.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 They that sat in the gate spoke against me: and they that drank wine made me their song.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 But as for me, my prayer is to thee, O Lord; for the time of thy good pleasure, O God. In the multitude of thy mercy hear me, in the truth of thy salvation.
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Draw me out of the mire, that I may not stick fast: deliver me from them that hate me, and out of the deep waters.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 Let not the tempest of water drown me, nor the deep swallow me up: and let not the pit shut her mouth upon me.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Hear me, O Lord, for thy mercy is kind; look upon me according to the multitude of thy tender mercies.
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 And turn not away thy face from thy servant: for I am in trouble, hear me speedily.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Attend to my soul, and deliver it: save me because of my enemies.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 Thou knowest my reproach, and my confusion, and my shame.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 In thy sight are all they that afflict me; my heart hath expected reproach and misery. And I looked for one that would grieve together with me, but there was none: and for one that would comfort me, and I found none.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 And they gave me gall for my food, and in my thirst they gave me vinegar to drink.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 Let their table become as a snare before them, and a recompense, and a stumblingblock.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Let their eyes be darkened that they see not; and their back bend thou down always.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Pour out thy indignation upon them: and let thy wrathful anger take hold of them.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 Let their habitation be made desolate: and let there be none to dwell in their tabernacles.
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 Because they have persecuted him whom thou hast smitten; and they have added to the grief of my wounds.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Add thou iniquity upon their iniquity: and let them not come into thy justice.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 Let them be blotted out of the book of the living; and with the just let them not be written.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 But I am poor and sorrowful: thy salvation, O God, hath set me up.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 I will praise the name of God with a canticle: and I will magnify him with praise.
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 And it shall please God better than a young calf, that bringeth forth horns and hoofs.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 Let the poor see and rejoice: seek ye God, and your soul shall live.
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 For the Lord hath heard the poor: and hath not despised his prisoners.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 Let the heavens and the earth praise him; the sea, and every thing that creepeth therein.
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 For God will save Sion, and the cities of Juda shall be built up. And they shall dwell there, and acquire it by inheritance.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 And the seed of his servants shall possess it; and they that love his name shall dwell therein.
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< Psalms 69 >