< Psalms 60 >

1 Unto the end, for them that shall be changed, for the inscription of a title, to David himself, for doctrine, When he set fire to Mesopotamia of Syria and Sobal and Joab returned and slew of Edom, in the vale of the saltpits, twelve thousand men. O God, thou hast cast us off, and hast destroyed us; thou hast been angry, and hast had mercy on us.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2 Thou hast moved the earth, and hast troubled it: heal thou the breaches thereof, for it has been moved.
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3 Thou hast shewn thy people hard things; thou hast made us drink wine of sorrow.
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4 Thou hast given a warning to them that fear thee: that they may flee from before the bow: That thy beloved may be delivered.
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
5 Save me with thy right hand, and hear me.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
6 God hath spoken in his holy place: I will rejoice, and I will divide Sichem; and will mete out the vale of tabernacles.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7 Galaad is mine, and Manasses is mine: and Ephraim is the strength of my head. Juda is my king:
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8 Moab is the pot of my hope. Into Edom will I stretch out my shoe: to me the foreigners are made subject.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9 Who will bring me into the strong city? who will lead me into Edom?
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10 Wilt not thou, O God, who hast cast us off? and wilt not thou, O God, go out with our armies?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11 Give us help from trouble: for vain is the salvation of man.
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12 Through God we shall do mightily: and he shall bring to nothing them that afflict us.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.

< Psalms 60 >