< Psalms 58 >

1 Unto the end, destroy not, for David, for an inscription of a title. If in very deed you speak justice: judge right things, ye sons of men.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 For in your heart you work iniquity: your hands forge injustice in the earth.
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 The wicked are alienated from the womb; they have gone astray from the womb: they have spoken false things.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 Their madness is according to the likeness of a serpent: like the deaf asp that stoppeth her ears:
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 Which will not hear the voice of the charmers; nor of the wizard that charmeth wisely.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 God shall break in pieces their teeth in their mouth: the Lord shall break the grinders of the lions.
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 They shall come to nothing, like water running down; he hath bent his bow till they be weakened.
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 Like wax that melteth they shall be taken away: fire hath fallen on them, and they shall not see the sun.
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Before your thorns could know the brier; he swalloweth them up, as alive, in his wrath.
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 The just shall rejoice when he shall see the revenge: he shall wash his hands in the blood of the sinner.
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 And man shall say: If indeed there be fruit to the just: there is indeed a God that judgeth them on the earth.
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”

< Psalms 58 >