< Psalms 57 >

1 Unto the end, destroy not, for David, for an inscription of a title, when he fled from Saul into the cave. Have mercy on me, O God, have mercy on me: for my soul trusteth in thee. And in the shadow of thy wings will I hope, until iniquity pass away.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
2 I will cry to God the most High; to God who hath done good to me.
Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
3 He hath sent from heaven and delivered me: he hath made them a reproach that trod upon me. God hath sent his mercy and his truth,
Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
4 And he hath delivered my soul from the midst of the young lions. I slept troubled. The sons of men, whose teeth are weapons and arrows, and their tongue a sharp sword.
Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
5 Be thou exalted, O God, above the heavens, and thy glory above all the earth.
Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
6 They prepared a snare for my feet; and they bowed down my soul. They dug a pit before my face, and they are fallen into it.
Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
7 My heart is ready, O God, my heart is ready: I will Sing, and rehearse a psalm.
Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
8 Arise, O my glory, arise psaltery and harp: I will arise early.
Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
9 I will give praise to thee, O Lord, among the people: I will sing a psalm to thee among the nations.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
10 For thy mercy is magnified even to the heavens: and thy truth unto the clouds.
Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
11 Be thou exalted, O God, above the heavens: and thy glory above all the earth.
Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.

< Psalms 57 >