< Psalms 55 >

1 Unto the end, in verses, understanding for David. Hear, O God, my prayer, and despise not my supplication:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Be attentive to me and hear me. I am grieved in my exercise; and am troubled,
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 At the voice of the enemy, and at the tribulation of the sinner. For they have cast iniquities upon me: and in wrath they were troublesome to me.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 My heart is troubled within me: and the fear of death is fallen upon me.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 Fear and trembling are come upon me: and darkness hath covered me.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 And I said: Who will give me wings like a dove, and I will fly and be at rest?
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 Lo, I have gone far off flying away; and I abode in the wilderness.
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 I waited for him that hath saved me from pusillanimity of spirit, and a storm.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Cast down, O Lord, and divide their tongues; for I have seen iniquity and contradiction in the city.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Day and night shall iniquity surround it upon its walls: and in the midst thereof are labour,
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 And injustice. And usury and deceit have not departed from its streets.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 For if my enemy had reviled me, I would verily have borne with it. And if he that hated me had spoken great things against me, I would perhaps have hidden myself from him.
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 But thou a man of one mind, my guide, and my familiar,
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 Who didst take sweetmeats together with me: in the house of God we walked with consent.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Let death come upon them, and let them go down alive into hell. For there is wickedness in their dwellings: in the midst of them. (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 But I have cried to God: and the Lord will save me.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Evening and morning, and at noon I will speak and declare: and he shall hear my voice.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 He shall redeem my soul in peace from them that draw near to me: for among many they were with me.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 God shall hear, and the Eternal shall humble them. For there is no change with them, and they have not feared God:
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 He hath stretched forth his hand to repay. They have defiled his covenant,
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 They are divided by the wrath Of his countenance, and his heart hath drawn near. His words are smoother than oil, and the same are darts.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Cast thy care upon the Lord, and he shall sustain thee: he shall not suffer the just to waver for ever.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 But thou, O God, shalt bring them down into the pit of destruction. Bloody and deceitful men shall not live out half their days; but I will trust in thee, O Lord.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Psalms 55 >