< Psalms 51 >

1 Unto the end, a psalm of David, When Nathan the prophet came to him after he had sinned with Bethsabee. Have mercy on me, O God, according to thy great mercy. And according to the multitude of thy tender mercies blot out my iniquity.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 Wash me yet more from my iniquity, and cleanse me from my sin.
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 For I know my iniquity, and my sin is always before me.
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 To thee only have I sinned, and have done evil before thee: that thou mayst be justified in thy words and mayst overcome when thou art judged.
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 For behold I was conceived in iniquities; and in sins did my mother conceive me.
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 For behold thou hast loved truth: the uncertain and hidden things of thy wisdom thou hast made manifest to me.
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 Thou shalt sprinkle me with hyssop, and I shall be cleansed: thou shalt wash me, and I shall be made whiter than snow.
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 To my hearing thou shalt give joy and gladness: and the bones that have been humbled shall rejoice.
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 Turn away thy face from my sins, and blot out all my iniquities.
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 Create a clean heart in me, O God: and renew a right spirit within my bowels.
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 Cast me not away from thy face; and take not thy holy spirit from me.
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 Restore unto me the joy of thy salvation, and strengthen me with a perfect spirit.
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 I will teach the unjust thy ways: and the wicked shall be converted to thee.
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 Deliver me from blood, O God, thou God of my salvation: and my tongue shall extol thy justice.
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 O Lord, thou wilt open my lips: and my mouth shall declare thy praise.
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 For if thou hadst desired sacrifice, I would indeed have given it: with burnt offerings thou wilt not be delighted.
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 A sacrifice to God is an afflicted spirit: a contrite and humbled heart, O God, thou wilt not despise.
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 Deal favourably, O Lord, in thy good will with Sion; that the walls of Jerusalem may be built up.
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 Then shalt thou accept the sacrifice of justice, oblations and whole burnt offerings: then shall they lay calves upon thy altar.
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.

< Psalms 51 >