< Psalms 50 >
1 A psalm for Asaph. The God of gods, the Lord hath spoken: and he hath called the earth. From the rising of the sun, to the going down thereof:
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 Out of Sion the loveliness of his beauty.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 God shall come manifestly: our God shall come, and shall not keep silence. A fire shall burn before him: and a mighty tempest shall be round about him.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 He shall call heaven from above, and the earth, to judge his people.
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 Gather ye together his saints to him: who set his covenant before sacrifices.
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 And the heavens shall declare his justice: for God is judge.
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 Hear, O my people, and I will speak: O Israel, and I will testify to thee: I am God, thy God.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 I will not reprove thee for thy sacrifices: and thy burnt offerings are always in my sight.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 I will not take calves out of thy house: nor he goats out of thy flocks.
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 For all the beasts of the woods are mine: the cattle on the hills, and the oxen.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 I know all the fowls of the air: and with me is the beauty of the field.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 If I should be hungry, I would not tell thee: for the world is mine, and the fulness thereof.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Shall I eat the flesh of bullocks? or shall I drink the blood of goats?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Offer to God the sacrifice of praise: and pay thy vows to the most High.
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 And call upon me in the day of trouble: I will deliver thee, and thou shalt glorify me.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 But to the sinner God hath said: Why dost thou declare my justices, and take my covenant in thy mouth?
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Seeing thou hast hated discipline: and hast cast my words behind thee.
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 If thou didst see a thief thou didst run with him: and with adulterers thou hast been a partaker.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Thy mouth hath abounded with evil, and thy tongue framed deceits.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Sitting thou didst speak against thy brother, and didst lay a scandal against thy mother’s son:
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 These things hast thou done, and I was silent. Thou thoughtest unjustly that I should be like to thee: but I will reprove thee, and set before thy face.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Understand these things, you that forget God; lest he snatch you away, and there be none to deliver you.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 The sacrifice of praise shall glorify me: and there is the way by which I will shew him the salvation of God.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”