< Psalms 49 >
1 Unto the end, a psalm for the sons of Core. Hear these things, all ye nations: give ear, all ye inhabitants of the world.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
2 All you that are earthborn, and you sons of men: both rich and poor together.
babba da yaro mai arziki da talaka.
3 My mouth shall speak wisdom: and the meditation of my heart understanding.
Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
4 I will incline my ear to a parable; I will open my proposition on the psaltery.
Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
5 Why shall I fear in the evil day? the iniquity of my heel shall encompass me.
Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
6 They that trust in their own strength, and glory in the multitude of their riches,
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7 No brother can redeem, nor shall man redeem: he shall not give to God his ransom,
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8 Nor the price of the redemption of his soul: and shall labour for ever,
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9 And shall still live unto the end.
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10 He shall not see destruction, when he shall see the wise dying: the senseless and the fool shall perish together: And they shall leave their riches to strangers:
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11 And their sepulchres shall be their houses for ever. Their dwelling places to all generations: they have called their lands by their names.
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12 And man when he was in honour did not understand; he is compared to senseless beasts, and is become like to them.
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
13 This way of theirs is a stumblingblock to them: and afterwards they shall delight in their mouth.
Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
14 They are laid in hell like sheep: death shall feed upon them. And the just shall have dominion over them in the morning; and their help shall decay in hell from their glory. (Sheol )
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
15 But God will redeem my soul from the hand of hell, when he shall receive me. (Sheol )
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
16 Be not thou afraid, when a man shall be made rich, and when the glory of his house shall be increased.
Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
17 For when he shall die he shall take nothing away; nor shall his glory descend with him.
gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
18 For in his lifetime his soul will be blessed: and he will praise thee when thou shalt do well to him.
Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
19 He shall go in to the generations of his fathers: and he shall never see light.
zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
20 Man when he was in honour did not understand: he hath been compared to senseless beasts, and made like to them.
Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.