< Psalms 40 >

1 Unto the end, a psalm for David himself. With expectation I have waited for the Lord, and he was attentive to me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
2 And he heard my prayers, and brought me out of the pit of misery and the mire of dregs. And he set my feet upon a rock, and directed my steps.
Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
3 And he put a new canticle into my mouth, a song to our God. Many shall see, and shall fear: and they shall hope in the Lord.
Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
4 Blessed is the man whose trust is in the name of the Lord; and who hath not had regard to vanities, and lying follies.
Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
5 Thou hast multiplied thy wonderful works, O Lord my God: and in thy thoughts there is no one like to thee. I have declared and I have spoken they are multiplied above number.
Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
6 Sacrifice and oblation thou didst not desire; but thou hast pierced ears for me. Burnt offering and sin offering thou didst not require:
Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
7 Then said I, Behold I come. In the head of the book it is written of me
Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
8 That I should do thy will: O my God, I have desired it, and thy law in the midst of my heart.
Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
9 I have declared thy justice in a great church, lo, I will not restrain my lips: O Lord, thou knowest it.
Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
10 I have not hid thy justice within my heart: I have declared thy truth and thy salvation. I have not concealed thy mercy and thy truth from a great council.
Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
11 Withhold not thou, O Lord, thy tender mercies from me: thy mercy and thy truth have always upheld me.
Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
12 For evils without number have surrounded me; my iniquities have overtaken me, and I was not able to see. They are multiplied above the hairs of my head: and my heart hath forsaken me.
Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
13 Be pleased, O Lord, to deliver me, look down, O Lord, to help me.
Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
14 Let them be confounded and ashamed together, that seek after my soul to take it away. Let them be turned backward and be ashamed that desire evils to me.
Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
15 Let them immediately bear their confusion, that say to me: Tis well, tis well.
Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
16 Let all that seek thee rejoice and be glad in thee: and let such as love thy salvation say always: The Lord be magnified.
Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
17 But I am a beggar and poor: the Lord is careful for me. Thou art my helper and my protector: O my God, be not slack.
Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.

< Psalms 40 >