< Psalms 4 >

1 Unto the end, in verses. A psalm for David. When I called upon him, the God of my justice heard me: when I was in distress, thou hast enlarged me. Have mercy on me: and hear my prayer.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
2 O ye sons of men, how long will you be dull of heart? why do you love vanity, and seek after lying?
Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
3 Know ye also that the Lord hath made his holy one wonderful: the Lord will hear me when I shall cry unto him.
Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
4 Be angry, and sin not: the things you say in your hearts, be sorry for them upon your beds.
Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
5 Offer up the sacrifice of justice, and trust in the Lord: many say, Who sheweth us good things?
Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
6 The light of thy countenance O Lord, is signed upon us: thou hast given gladness in my heart.
Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
7 By the fruit of their corn, their wine and oil, they are multiplied.
Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
8 In peace in the selfsame I will sleep, and I will rest: For thou, O Lord, singularly hast settled me in hope.
Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.

< Psalms 4 >