< Psalms 38 >
1 A psalm for David, for a remembrance of the sabbath. Rebuke me not, O Lord, in thy indignation; nor chastise me in thy wrath.
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 For thy arrows are fastened in me: and thy hand hath been strong upon me.
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3 There is no health in my flesh, because of thy wrath: there is no peace for my bones, because of my sins.
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4 For my iniquities are gone over my head: and as a heavy burden are become heavy upon me.
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5 My sores are putrified and corrupted, because of my foolishness.
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6 I am become miserable, and am bowed down even to the end: I walked sorrowful all the day long.
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7 For my loins are filled with illusions; and there is no health in my flesh.
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8 I am afflicted and humbled exceedingly: I roared with the groaning of my heart.
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
9 Lord, all my desire is before thee, and my groaning is not hidden from thee.
Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
10 My heart is troubled, my strength hath left me, and the light of my eyes itself is not with me.
Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
11 My friends and my neighbours have drawn near, and stood against me. And they that were near me stood afar off:
Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
12 And they that sought my soul used violence. And they that sought evils to me spoke vain things, and studied deceits all the day long.
Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 But I, as a deaf man, heard not: and as a dumb man not opening his mouth.
Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
14 And I became as a man that heareth not: and that hath no reproofs in his mouth.
Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
15 For in thee, O Lord, have I hoped: thou wilt hear me, O Lord my God.
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16 For I said: Lest at any time my enemies rejoice over me: and whilst my feet are moved, they speak great things against me.
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17 For I am ready for scourges: and my sorrow is continually before me.
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18 For I will declare my inequity: and I will think for my sin.
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19 But my enemies live, and are stronger that I: and they hate me wrongfully are multiplied.
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20 They that render evil for good, have detracted me, because I followed goodness.
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
21 Forsake me not, O Lord my God: do not thou depart from me.
Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
22 Attend unto my help, O Lord, the God of my salvation.
Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.