< Psalms 25 >
1 Unto the end, a psalm for David. To thee, O Lord, have I lifted up my soul.
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 In thee, O my God, I put my trust; let me not be ashamed.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Neither let my enemies laugh at me: for none of them that wait on thee shall be confounded.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Let all them be confounded that act unjust things without cause. Shew, O Lord, thy ways to me, and teach me thy paths.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Direct me in thy truth, and teach me; for thou art God my Saviour; and on thee have I waited all the day long.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Remember, O Lord, thy bowels of compassion; and thy mercies that are from the beginning of the world.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 The sins of my youth and my ignorances do not remember. According to thy mercy remember thou me: for thy goodness’ sake, O Lord.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 The Lord is sweet and righteous: therefore he will give a law to sinners in the way.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 He will guide the mild in judgment: he will teach the meek his ways.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 All the ways of the Lord are mercy and truth, to them that seek after his covenant and his testimonies.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 For thy name’s sake, O Lord, thou wilt pardon my sin: for it is great.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 Who is the man that feareth the Lord? He hath appointed him a law in the way he hath chosen.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 His soul shall dwell in good things: and his seed shall inherit the land.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 The Lord is a firmament to them that fear him: and his covenant shall be made manifest to them.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 My eyes are ever towards the Lord: for he shall pluck my feet out of the snare.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Look thou upon me, and have mercy on me; for I am alone and poor.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 The troubles of my heart are multiplied: deliver me from my necessities.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 See my abjection and my labour; and forgive me all my sins.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Consider my enemies for they are multiplied, and have hated me with an unjust hatred.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Keep thou my soul, and deliver me: I shall not be ashamed, for I have hoped in thee.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 The innocent and the upright have adhered to me: because I have waited on thee.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 Deliver Israel, O God, from all his tribulations.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!