< Psalms 22 >
1 Unto the end, for the morning protection, a psalm for David. O God my God, look upon me: why hast thou forsaken me? Far from my salvation are the words of my sins.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 O my God, I shall cry by day, and thou wilt not hear: and by night, and it shall not be reputed as folly in me.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 But thou dwellest in the holy place, the praise of Israel.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 In thee have our fathers hoped: they have hoped, and thou hast delivered them.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 They cried to thee, and they were saved: they trusted in thee, and were not confounded.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 But I am a worm, and no man: the reproach of men, and the outcast of the people.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 All they that saw me have laughed me to scorn: they have spoken with the lips, and wagged the head.
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 He hoped in the Lord, let him deliver him: let him save him, seeing he delighteth in him.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 For thou art he that hast drawn me out of the womb: my hope from the breasts of my mother.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 I was cast upon thee from the womb. From my mother’s womb thou art my God,
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Depart not from me. For tribulation is very near: for there is none to help me.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Many calves have surrounded me: fat bulls have besieged me.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 They have opened their mouths against me, as a lion ravening and roaring.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 I am poured out like water; and all my bones are scattered. My heart is become like wax melting in the midst of my bowels.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 My strength is dried up like a potsherd, and my tongue hath cleaved to my jaws: and thou hast brought me down into the dust of death.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 For many dogs have encompassed me: the council of the malignant hath besieged me. They have dug my hands and feet.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 They have numbered all my bones. And they have looked and stared upon me.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 They parted my garments amongst them; and upon my vesture they cast lots.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 But thou, O Lord, remove not thy help to a distance from me; look towards my defence.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Deliver, O God, my soul from the sword: my only one from the hand of the dog.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Save me from the lion’s mouth; and my lowness from the horns of the unicorns.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 I will declare thy name to my brethren: in the midst of the church will I praise thee.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Ye that fear the Lord, praise him: all ye the seed of Jacob, glorify him.
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Let all the seed of Israel fear him: because he hath not slighted nor despised the supplication of the poor man. Neither hath he turned away his face from me: and when I cried to him he heard me.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 With thee is my praise in a great church: I will pay my vows in the sight of them that fear him.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 The poor shall eat and shall be filled: and they shall praise the Lord that seek him: their hearts shall live for ever and ever.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 All the ends of the earth shall remember, and shall be converted to the Lord: And all the kindreds of the Gentiles shall adore in his sight.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 For the kingdom is the Lord’s; and he shall have dominion over the nations.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 All the fat ones of the earth have eaten and have adored: all they that go down to the earth shall fall before him.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 And to him my soul shall live: and my seed shall serve him.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 There shall be declared to the Lord a generation to come: and the heavens shall shew forth his justice to a people that shall be born, which the Lord hath made.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.