< Psalms 125 >

1 They that trust in the Lord shall be as mount Sion: he shall not be moved for ever that dwelleth
Waƙar haurawa. Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona, wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.
2 In Jerusalem. Mountains are round about it: so the Lord is round about his people from henceforth now and for ever.
Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima, haka Ubangiji ya kewaye mutanensa yanzu da har abada kuma.
3 For the Lord will not leave the rod of sinners upon the lot of the just: that the just may not stretch forth their hands to iniquity.
Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance a kan ƙasar da take rabon adalai ba, domin kada masu adalci su yi amfani da hannuwansu su aikata mugunta.
4 Do good, O Lord, to those that are good, and to the upright of heart.
Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu, ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.
5 But such as turn aside into bonds, the Lord shall lead out with the workers of iniquity: peace upon Israel.
Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta. Salama tă kasance tare da Isra’ila.

< Psalms 125 >