< Psalms 115 >
1 Not to us, O Lord, not to us; but to thy name give glory.
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 For thy mercy, and for thy truth’s sake: lest the gentiles should say: Where is their God?
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 But our God is in heaven: he hath done all things whatsoever he would.
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 The idols of the gentiles are silver and gold, the works of the hands of men.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 They have mouths and speak not: they have eyes and see not.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 They have ears and hear not: they have noses and smell not.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 They have hands and feel not: they have feet and walk not: neither shall they cry out through their throat.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Let them that make them become like unto them: and all such as trust in them.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 The house of Israel hath hoped in the Lord: he is their helper and their protector.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 The house of Aaron hath hoped in the Lord: he is their helper and their protector.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 They that fear the Lord hath hoped in the Lord: he is their helper and their protector.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 The Lord hath been mindful of us, and hath blessed us. He hath blessed the house of Israel: he hath blessed the house of Aaron.
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 He hath blessed all that fear the Lord, both little and great.
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 May the Lord add blessings upon you: upon you, and upon your children.
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 Blessed be you of the Lord, who made heaven and earth.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 The heaven of heaven is the Lord’s: but the earth he has given to the children of men.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 The dead shall not praise thee, O Lord: nor any of them that go down to hell. ()
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 But we that live bless the Lord: from this time now and for ever.
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.