< Psalms 110 >
1 The Lord said to my Lord: Sit thou at my right hand: Until I make thy enemies thy footstool.
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
2 The Lord will send forth the sceptre of thy power out of Sion: rule thou in the midst of thy enemies.
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
3 With thee is the principality in the day of thy strength: in the brightness of the saints: from the womb before the day star I begot thee.
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
4 The Lord hath sworn, and he will not repent: Thou art a priest for ever according to the order of Melchisedech.
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
5 The Lord at thy right hand hath broken kings in the day of his wrath.
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
6 He shall judge among nations, he shall fill ruins: he shall crush the heads in the land of the many.
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
7 He shall drink of the torrent in the way: therefore shall he lift up the head.
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.