< Proverbs 5 >
1 My son, attend to my wisdom, and incline thy ear to my prudence.
Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
2 That thou mayst keep thoughts, and thy lips may preserve instruction. Mind not the deceit of a woman.
don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
3 For the lips of a harlot are like a honeycomb dropping, and her throat is smoother than oil.
Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
4 But her end is bitter as wormwood, and sharp as a two-edged sword.
amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
5 Her feet go down into death, and her steps go in as far as hell. (Sheol )
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol )
6 They walk not by the path of life, her steps are wandering, and unaccountable.
Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
7 Now therefore, my son, hear me, and depart not from the words of my mouth.
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
8 Remove thy way far from her, and come not nigh the doors of her house.
Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
9 Give not thy honour to strangers, and thy years to the cruel.
don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
10 Lest strangers be filled with thy strength, and thy labours be in another man’s house,
don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
11 And thou mourn it the last, when thou shalt have spent thy flesh and thy body, and say:
A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
12 Why have I hated instruction, and my heart consented not to reproof,
Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
13 And have not heard the voice of them that taught me, and have not inclined my ear to masters?
Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
14 I have almost been in all evil, in the midst of the church and of the congregation.
Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
15 Drink water out of thy own cistern, and the streams of thy own well:
Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
16 Let thy fountains be conveyed abroad, and in the streets divide thy waters.
In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
17 Keep them to thyself alone, neither let strangers be partakers with thee.
Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
18 Let thy vein be blessed, and rejoice with the wife of thy youth:
Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
19 Let her be thy dearest hind, and most agreeable fawn: let her breasts inebriate thee at all times; he thou delighted continually with her love.
Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
20 Why art thou seduced, my son, by a strange woman, and art cherished in the bosom of another?
Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
21 The Lord beholdeth the ways of man, and considereth all his steps.
Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
22 His own iniquities catch the wicked, and he is fast bound with the ropes of his own sins.
Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
23 He shall die, because he hath not received instruction, and in the multitude of his folly he shall be deceived.
Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.