< Proverbs 20 >

1 Wine is a luxurious thing, and drunkenness riotous: whosoever is delighted therewith shell not be wise.
Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
2 As the roaring of a lion, so also is the dread of a king: he that provoketh him, sinneth against his own soul.
Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
3 It is an honour for a man to separate himself from quarrels: but all fools are meddling with reproaches.
Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
4 Because of the cold the sluggard would not plough: he shall beg therefore in the summer, and it shall not be given him.
Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
5 Counsel in the heart of a man is like deep water: but a wise man will draw it out.
Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
6 Many men are called merciful: but who shall find a faithful man?
Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
7 The just that walketh in his simplicity, shall leave behind him blessed children.
Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
8 The king, that sitteth on the throne of judgment, scattereth away all evil with his look.
Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
9 Who can say: My heart is clean, I am pure from sin?
Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
10 Diverse weights and diverse measures, both are abominable before God.
Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
11 By his inclinations a child is known, if his works be clean and right.
Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
12 The hearing ear, and the seeing eye, the Lord hath made them both.
Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
13 Love not sleep, lest poverty oppress thee: open thy eyes, and be filled with bread.
Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
14 It is nought, it is nought, saith every buyer: and when he is gone away, then he will boast.
“Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
15 There is gold, and a multitude of jewels: but the lips of knowledge are a precious vessel.
Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
16 Take away the garment of him that is surety for a stranger, and take a pledge from him for strangers.
A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
17 The bread of lying is sweet to a man: but afterwards his mouth shall be filled with gravel.
Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
18 Designs are strengthened by counsels: and wars are to be managed by governments.
Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
19 Meddle not with him that revealeth secrets, and walketh deceitfully, and openeth wide his lips.
Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
20 He that curseth his father, and mother, his lamp shall be put out in the midst of darkness.
In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
21 The inheritance gotten hastily in the beginning, in the end shall be without a blessing.
Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
22 Say not: I will return evil: wait for the Lord and he will deliver thee.
Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
23 Diverse weights are an abomination before the Lord: a deceitful balance is not good.
Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
24 The steps of man are guided by the Lord: but who is the man that can understand his own way?
Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
25 It is ruin to a man to devour holy ones, and after vows to retract.
Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
26 A wise king scattereth the wicked, and bringeth over them the wheel.
Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
27 The spirit of a man is the lamp of the Lord, which searcheth all the hidden things of the bowels.
Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
28 Mercy and truth preserve the king, and his throne is strengthened by clemency.
Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
29 The joy of young men is their strength: and the dignity of old men, their grey hairs.
Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
30 The blueness of a wound shall wipe away evils: and stripes in the more inward parts of the belly.
Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.

< Proverbs 20 >