< Proverbs 2 >
1 My son, if thou wilt receive my words, and wilt hide my commandments with thee,
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 That thy ear may hearken to wisdom: Incline thy heart to know prudence:
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 For if thou shalt call for wisdom, and incline thy heart to prudence:
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 If thou shalt seek her as money, and shalt dig for her as for a treasure:
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Then shalt thou understand the fear of the Lord, and shalt find the knowledge of God.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Because the Lord giveth wisdom: and out of his mouth cometh prudence and knowledge.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 He will keep the salvation of the righteous, and protect them that walk in simplicity.
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 Keeping the paths of justice, and guarding the ways of saints.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Then shalt thou understand justice, and judgment, and equity, and every good path.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 If wisdom shall enter into thy heart, and knowledge please thy soul:
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Counsel shall keep thee, and prudence shall preserve thee,
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 That thou mayst be delivered from the evil way, and from the man that speaketh perverse things:
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 Who leave the right way, and walk by dark ways:
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Who are glad when they have done evil, and rejoice in most wicked things:
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Whose ways are perverse, and their steps infamous.
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 That thou mayst be delivered from the strange women, and from the stranger, who softeneth her words:
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 And forsaketh the guide of her youth,
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 And hath forgotten the covenant of her God: for her house inclineth unto death, and her paths to hell. ()
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 None that go in unto her shall return again, neither shall they take hold of the paths of life,
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 That thou mayst walk in a good way: and mayst keep the paths of the just.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 For they that are upright shall dwell in the earth, and the simple shall continue in it.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 But the wicked shall be destroyed from the earth: and they that do unjustly shall be taken away from it.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.