< Numbers 21 >

1 And when king Arad the Chanaanite, who dwelt towards the south, had heard this, to wit, that Israel was come by the way of the spies, he fought against them, and overcoming them carried off their spoils.
Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
2 But Israel binding himself by vow to the Lord, said: It thou wilt deliver this people into my hand, I will utterly destroy their cities.
Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
3 And the Lord heard the prayers of Israel, and delivered up the Chanaanite, and they cut them off and destroyed their cities: and they called the name of that place Horma, that is to say, Anathema.
Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
4 And they marched from mount Hor, by the way that leadeth to the Red Sea, to compass the land of Edom. And the people began to be weary of their journey and labour:
Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
5 And speaking against God and Moses, they said: Why didst thou bring us out of Egypt, to die in the wilderness? There is no bread, nor have we any waters: our soul now loatheth this very light food.
suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
6 Wherefore the Lord sent among the people fiery serpents, which bit them and killed many of them.
Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
7 Upon which they came to Moses, and said: We have sinned, because we have spoken against the Lord and thee: pray that he may take away these serpents from us. And Moses prayed for the people.
Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
8 And the Lord said to him: Make brazen serpent, and set it up for a sign: whosoever being struck shall look on it, shall live.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
9 Moses therefore made a brazen serpent, and set it up for a sign: which when they that were bitten looked upon, they were healed.
Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
10 And the children of Israel setting forwards camped in Oboth.
Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
11 And departing thence they pitched their tents in Jeabarim, in the wilderness, that faceth Moab toward the east.
Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
12 And removing from thence, they came to the torrent Zared:
Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
13 Which they left and encamped over against Arnon, which is in the desert and standeth out on the borders of the Amorrhite. For Arnon is the border of Moab, dividing the Moabites and the Amorrhites.
Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
14 Wherefore it is said in the book of the wars of the Lord: As he did in the Red Sea, so will he do in the streams of Amen.
Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
15 The rocks of the torrents were bowed down that they might rest in Ar, and lie down in the borders of the Moabites.
da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
16 When they went from that place, the well appeared whereof the Lord said to Moses: Gather the people together, and I will give them water.
Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
17 Then Israel sung this song: Let the well spring up. They sung thereto:
Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
18 The well, which the princes dug, and the chiefs of the people prepared by the direction of the lawgiver, and with their staves. And they marched from the wilderness to Mathana.
game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
19 From Mathana unto Nahaliel: from Nahaliel unto Bamoth.
daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
20 From Bamoth, is a valley in the country of Moab, to the top of Phasga, which looked towards the desert.
daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
21 And Israel sent messengers to Sehon king of the Amorrhites, saying:
Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
22 I beseech thee that I may have leave to pass through thy land: we will not go aside into the fields or the vineyards, we will not drink waters of the wells, we will go the king’s highway, till we be past thy borders.
“Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
23 And he would not grant that Israel should pass by his borders: but rather gathering an army, went forth to meet them in the desert, and came to Jasa, and fought against them.
Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
24 And he was slain by them with the edge of the sword, and they possessed his land from the Arnon unto the Jeboc, and to the confines of the children of Ammon: for the borders of the Ammonites, were kept with a strong garrison.
Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
25 So Israel took all his cities, and dwelt in the cities of the Amorrhite, to wit, in Hesebon, and in the villages thereof.
Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
26 Hesebon was the city of Sehon the king of the Amorrhites, who fought against the king of Moab: and took all the land, that had been of his dominions, as far as the Arnon.
Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
27 Therefore it is said in the proverb: Come into Hesebon, let the city of Sehon be built and set up:
Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
28 A fire is gone out of Hesebon, a flame from the city of Sehon, and hath consumed Ar of the Moabites, and the inhabitants of the high places of the Arnon.
“Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
29 Woe to thee Moab: thou art undone, O people of Chamos. He hath given his sons to flight, and his daughters into captivity to Sehon the king of the Amorrhites.
Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
30 Their yoke is perished from Hesebon unto Dibon, they came weary to Nophe, and unto Medaba.
“Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
31 So Israel dwelt in the land of the Amorrhite.
Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
32 And Moses sent some to take a view of Jazer: and they took the villages of it, and conquered the inhabitants.
Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
33 And they turned themselves, and went up by the way of Basan, and Og the king of Basan came against them with all his people, to fight in Edrai.
Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
34 And the Lord said to Moses: Fear him not, for I have delivered him and all his people, and his country into thy hand: and thou shalt do to him as thou didst to Sehon the king of the Amorrhites, the inhabitant of Hesebon.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
35 So they slew him also with his sons, and all his people, not letting any one escape, and they possessed his land.
Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.

< Numbers 21 >